Babban Jami'i a Gwamnatin Bauchi Ya Rasu a Makkah ana Shirin Fara Aikin Hajji
- Gwamnatin jihar Bauchi ta tabbatar da rasuwar daya daga cikin jami'anta a kasar Saudiyya wanda ya je aikin hajji
- Marigayin wanda shi ne babban sakataren musamman a ofishin Sakataren Gwamnatin jihar ya rasu bayan jinya
- Marigayin wanda aka fi sani da Turakin Dawakin Misau ya rasu ne ana saura kwanaki kadan a fara aiki hajj a Saudiyya
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.
Bauchi - Gwamna Bala Mohammed ya jajanta wa iyalai da abokan aikin daya daga cikin jami'an gwamnatinsa da ya rasu a Saudiyya.
Marigayin, Alhaji Shehu Yahaya Jalam shi ne babban sakatare mai kula da ayyuka na musamman a ofishin sakataren gwamnatin Bauchi.
A cikin wata sanarwa da mai ba gwamna Bala Mohammed shawara kan yada labarai, Mukhtar Gidado ya fitar, gwamnatin Bauchi ta bayyana rasuwar da matukar alhini.

Kara karanta wannan
Bayan sun yi barazana, gwamnatin tarayya ta amince da karin alawus na 40% ga ma’aikata
Rahotanni sun bayyana cewa marigayin ya rasu ne da safiyar Lahadi bayan gajeruwar rashin lafiya yayin da yake cikin tawagar alhazan Bauchi a Saudiyya.
Marigayin wanda ke rike da sarautar Turakin Dawakin Misau ya kasance daya daga cikin jami’an gwamnati masu taimakawa wajen tsara ayyukan hajji da sauran harkokin gwamnati.
Sanarwar ta ce marigayin ma’aikaci ne mai kwazo, biyayya da sadaukarwa wanda ya bayar da rayuwarsa wajen yi wa gwamnatin Bauchi hidima tsawon shekaru.
Mukhtar Gidado ya ce rasuwar tasa babban gibi ba ga iyalansa kadai ba, har ma da gwamnati da al’ummar da suka amfana da kwarewarsa.
An gudanar da sallar jana’izarsa ne bayan sallar Azahar a masallacin Ka’aba da ke birnin Makkah ranar Lahadi bayan tabbatar da rasuwarsa.
Gwamna Bala Mohammed ya mika sakon ta’aziyya ga iyalansa, ofishin sakataren gwamnatin Bauchi, shugaban ma’aikata, masarautun Misau da Dambam da sauran abokan hulda.
Gwamnan ya kuma yi addu’ar Allah ya gafarta kura-kuransa, ya sanya shi cikin Aljannatul Firdaus tare da bai wa iyalansa hakurin jure rashin.
Ƙarin bayani na tafe. ...
Asali: Legit.ng