Hajjin Bana
Gwamna Umar Namadi na jihar Jigawa da ke Arewacin Najeriya ya ba maniyyatan jiharsa N1m bayan hukumar alhazai ta kara N1.9m a kowace kujera hajjjn bana.
Gwamnatin tarayya karƙashin shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ta ba ɗa N90bn domin ragewa ƴan Najeriya kuɗin kujerar hajjin bana 2024 in ji majiya.
Gwamna Bala Mohammed na jihar Bauchi ya tallafawa maniyyatan jiharsa da rabin kuɗin da NAHCON ta ƙarawa maniyyatan jiharsa, ya ba da sabon umarni.
Gwamnan jihar Ribas, Siminalayi Fubara ya biya wa maniyyatan jiharsa Musulmai cikon kudin kumar hajji har N1.9m kan kowace kujera bayan hukumar alhazai ta kara kuɗi.
Wasu gwamnonin jihohi sun ba da tallafin kudi ga alhazai domin taimaka musu wajen cikata kudaden aikin hajjin su biyo bayan karin kudin da NAHCON ta yi.
Yayin da ake kukan tsadar kuɗin zuwa sauke farali, mun tattara muku yadda musulman Najeriya suka biya kuɗin hajji tun daga 2015 zuwa shekarar da muke ciki.
Sanata Ali Ndume ya yi Allah wadai da karin kudin kujerar aikin hajji inda ya bukaci Shugaba Bola Tinubu da ya biya cikon kudin ga maniyyata domin rage musu wahala.
Gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar Kano ya sanar da bayar da tallafin N500,000 ga kowane maniyyaci da ke shirin zuwa aikin hajjin 2024 a jihar, bayan karin kudin Hajj.
Rahotanni daga wasu jihohin Najeriya sun nuna yadɗa maniyyata ke zuwa neman a dawo masu da kuɗaɗensu bayan NAHCON ta sanar da ƙarin N1.9m a kowace kujera.
Hajjin Bana
Samu kari