Danjuma, Dangote, BUA Sun Yi Gasar Kudi a Wani Babban Taro da Aka Shirya a Abuja
- Tsohon ministan tsaro, Janar Theophilus Danjuma mai ritaya, ya bayar da gudunmawar Naira biliyan uku wajen kaddamar da littafin tarihin Yakubu Gowon
- Attajirin Afrika, Aliko Dangote, shi ma ya bayar da Naira miliyan 500 domin sayen kwafe 25 na littafin tarihin tsohon shugaban kasar
- Kashim Shettima da manyan jami’an gwamnati da na soja sun halarci taron kaddamar da littafin da aka gudanar a Abuja
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Sani Hamza ƙwararren edita ne a fannin nishaɗi, al'amuran yau da kullum, da kuma siyasa, wanda ke da shekaru sama da biyar a aikin jarida.
Abuja - Tsohon ministan tsaro, Janar Theophilus Danjuma mai ritaya, ya bayar da gudunmawar Naira biliyan uku yayin kaddamar da littafin tarihin tsohon shugaban kasa, Janar Yakubu Gowon mai ritaya.
Rahoto ya nuna cewa shugaban rukunin kamfanonin Dangote, Alhaji Aliko Dangote, shi ma ya bayar da gudunmawar Naira miliyan 500 wajen tallafa wa taron kaddamar da littafin.

Kara karanta wannan
Mutane sun barke da dariya da Jonathan ya kira Sarkin Kano Sanusi II da wani suna a taro

Source: Twitter
An kaddamar da littafin rayuwar Gowon
Kamfanin dillancin labarai na Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa an gudanar da bikin gabatar da littafin mai taken “My Life of Duty and Allegiance” ne a birnin tarayya Abuja.
Littafin ya kunshi babi 20 tare da halartar mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima, wanda ya wakilci shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, kamar yadda rahoton ya nuna.
Rahotanni sun nuna cewa manyan jami’an gwamnati, jakadu, manyan hafsoshin soja da sauran manyan baki sun halarci bikin da aka gudanar a babban birnin tarayya Abuja.
Danjuma, wanda shi ne babban mai gabatar da littafin, ya samu wakilcin tsohon babban hafsan tsaro, Janar Martin Luther Agwai mai ritaya.
Baya ga bayar da kudin tallafi, Danjuma ya umurci a sayi kwafe 12 na littafin domin rabawa dakunan karatu na jami’o’i 20 da suka taba bai wa Gowon digirin girmamawa.
Danjuma ya yabawa Gowon
A jawabin da aka karanta a madadinsa, Danjuma ya bayyana Gowon a matsayin daya daga cikin manyan dattawan Najeriya da suka yi fice a duniya.
Ya ce Gowon ya taka muhimmiyar rawa wajen hana Najeriya tarwatsewa a lokacin yakin basasa, yana mai cewa:
“Janar Gowon ba sanannen suna ba ne kawai a Najeriya, shi babban jagora ne da duniya ta amince da shi saboda kwarewa wajen shugabanci da gina kasa.”
Dangote ya bayar da N500m
Wakilin Aliko Dangote, Mansur Ahmed, ya bayyana cewa attajirin ya sayi kwafi 25 na littafin kan Naira miliyan 500 domin girmama Gowon.
Ahmed ya ce Dangote yana dan shekara 10 ne kawai lokacin da Gowon yake shugabantar Najeriya a lokacin mawuyacin hali.
Ya bayyana cewa kokarin Gowon na tabbatar da hadin kan Najeriya ne ya samar da yanayin da ya bai wa Dangote damar gina babbar daular kasuwanci a Afrika.
BUA da sauran attajirai sun tallafa
Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa sauran attajirai da manyan baki da suka halarci tron sun sayi kwafin littafin da makudan kudade.
Daga ciki akwai shugaban rukunin kamfanonin BUA, Abdul Samad Rabiu, wanda ya sayi kwafi na Naira miliyan 25.
An kuma bayyana cewa fitaccen malamin cocin Katolika kuma mai sharhi kan al’amuran yau da kullum, Bishop Mathew Kukah, ne ya yi bitar littafin a wajen taron.
Asali: Legit.ng
