'Babban Kuskure da Ƴan Najeriya Za Su Yi idan Suka Gujewa Zaɓen Tinubu a 2027'
- Shugaban Majalisar Wakilai, Tajudeen Abbas, ya ce rashin sake zaɓen Shugaba Tinubu a 2027 zai zama babban kuskure ga ’yan Najeriya
- Ya bukaci ƙungiyar PBAT Door-to-Door Movement ta yi kamfen bisa hujjoji da ƙididdigar ayyukan gwamnatin Tinubu tun bayan hawanta mulki a 2023
- Ƙungiyar, wadda Tompolo ke jagoranta, ta ce tana son tattara aƙalla kuri’u miliyan 10 domin tabbatar da nasarar Tinubu a 2027
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.
Abuja - Shugaban Majalisar Wakilan Najeriya, Rt. Hon. Abbas Tajudeen, ya yi magana game da zaben Bola Tinubu a 2027.
Kakakin Majalisar ya gargadi ’yan Najeriya cewa zaɓen wani ɗan takara a 2027 na iya zama babban kuskure.

Source: Twitter
Tajudeen ya bayyana haka ne a Abuja ranar Laraba, yayin da yake jawabi ga tawagar PBAT Door-to-Door Movement da ta kai masa ziyara, cewar Tribune.

Kara karanta wannan
Sanatocin APC sun jajubo rigima da jam'iyyar, an ba su wa'adi su gyara alaka da ita
Tajudeen Abbas ya yaba salon mulkin Tinubu
Ya ce zai zama rashin adalci idan ’yan Najeriya suka jure tsare-tsare da manufofin gwamnatin Tinubu, sannan su zaɓi wani shugaban da zai soke su.
Ya bukaci ƙungiyar ta gudanar da kamfen domin sake zaɓen Shugaba Bola Tinubu bisa la’akari da ƙididdigar ayyukan gwamnatin yanzu.
Ya ce zai kasance mai sauƙi a gabatar da ɗan takarar jam’iyyar All Progressives Congress, APC, ga ’yan Najeriya tare da samun sama da kuri’u miliyan 10.
Tajudeen ya bayyana cewa kamfen ɗin sake zaɓen Tinubu zai fi karkata ne kan hujjoji da ƙididdiga da ke nuna irin ci gaban da gwamnati ta samu tun 2023.
Tajudeen ya ce:
“Wannan kamfen ya kamata ya kasance bisa hujjoji da ƙididdiga. A bar mutane su ga kuma su ji irin abubuwan da gwamnati ta cimma cikin shekaru ukun da suka gabata.
“Kuma ba zai kasance abu mai wahala ba, domin duk mun san abin da wannan gwamnati ta yi a jihohi 36 na ƙasar nan.
“Saboda haka, kamfen ɗin zai kasance bisa hikima, balaga, hujjoji da ƙididdiga. Matukar kuka tsaya kan waɗannan abubuwa biyar, ba za ku yi kuskure ba.”

Source: Facebook
Kokarin da Tinubu ya yi a Najeriya
Shugaban Majalisar Wakilan ya ce babu wata hukuma a matakin tarayya da ta fi Majalisar Wakilai kusanci da talakawa.
Ya ce majalisar za ta ci gaba da wayar da kan jama’a kan muhimmancin ci gaba da mulkin gwamnatin Tinubu, cewar Daily Post.
Tajudeen ya ce:
"Ina tabbatar muku cewa za mu ci gaba da kasancewa cikin jakadun da za su wayar da kan jama’a game da hikimar ci gaba da mulki.
“Domin a ƙasar da aka yi shekaru sama da 40 cikin shekaru 60 na tarihinta ana tafiyar da ita ba daidai ba, babu shugaban da zai iya gyara duk kura-kuran baya cikin shekaru huɗu.
“Saboda haka, zai zama babban kuskure idan ’yan Najeriya suka mayar da baya kan ƙananan nasarorin da aka samu daga 2023 zuwa yanzu."
Za a kai tallan Tinubu Kano
Mun ji cewa wani kwamitin tallafa wa mazauna Kano ya shirya ƙaddamar da shirin ƙarfafa tattalin arziki domin samun goyon bayan Bola Tinubu.

Kara karanta wannan
2027: Matawalle ya fito fili ya bayyana irin zaben da za a yi karkashin gwamnatin Tinubu
Shirin da Leke Abejide ke jagoranta zai tallafa wa matasa, mata, ’yan kasuwa, masu sana’o’i da ƙananan ’yan kasuwa a faɗin Kano.
Kwamitin ya ce shirin ba siyasa kawai yake nufi ba, zai samar da damarmaki, ƙarfafa al’umma da kuma ƙara shiga cikin harkokin dimokuraɗiyya.
Asali: Legit.ng
