Ana cikin Sukar Kalaman Shekh Jingir, ADC Ta Tsaida Tikitin Takarar Musulmi da Musulmi a 2027

Ana cikin Sukar Kalaman Shekh Jingir, ADC Ta Tsaida Tikitin Takarar Musulmi da Musulmi a 2027

  • Jam'iyyar ADC ta tsayar da Hon Mamman Musa daga Bosso a matsayin dan takarar mataimakin gwamna a jihar Neja
  • Matakin ya zo ne duk da kiran wasu matasan Kiristoci na kauce wa zaɓar ’yan takarar da za su hada tikitin Musulmi da Musulmi
  • Kpautagi ya ce gwamnatinsa za ta mayar da hankali kan tsaro, noma, kasuwanci da samar da ayyukan yi ga matasa

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Niger, Nigeria - Sabanin abin da wasu matasan Kiristoci a jihar Neja ke tsammani, ɗan takarar gwamnan jam’iyyar ADC, Alhaji Mohammed Kpautagi, ya zaɓi Musulmi a matsayin abokin takararsa a zaɓen 2027.

Kpautagi ya bayyana tsohon Kwamishinan Ayyuka, Alhaji Mamman Musa daga Bosso, a matsayin ɗan takararsa na mataimakin gwamna.

Mohammed Kpautagi.
Dan takarar gwamnan jihar Neja a zaben 2027 karkashin inuwar jam'iyyar ADC, Mohammed Kpautagi Hoto: Dr. Mohammed Kpautagi
Source: Facebook

Jaridar Leadership ta rahoto cewa matakin ya zo ne bayan wasu matasan Kiristoci sun yi barazanar kin zaɓar duk wani ɗan takarar gwamna da zai fito da tikitin Musulmi da Musulmi.

Kara karanta wannan

Dan takarar NDC: 'Abin da ya sa Najeriya ke bukatar Obi da Kwankwaso'

Matasan Kiristoci ba su yi tsammani ba

Wasu matasan Kiristoci sun nuna adawa da tikitin Musulmi da Musulmi musamman bayan gwamnan Neja kuma ɗan takarar APC, Mohammed Umaru Bago, ya zaɓi Musulmi a matsayin abokin takararsa.

Saboda haka, akwai tsammanin cewa ADC za ta zaɓi Kirista a matsayin mataimakin Kpautagi domin samar da tikitin da ya bambanta da na APC.

Sai dai hakan bai ssmu ba, bayan Kpautagi ya bayyana Alhaji Mamman Musa, wanda shi ma Musulmi ne, a matsayin abokin takararsa.

Kpautagi ya kare zabinsa

Da yake bayyana dalilin zaɓar Mamman Musa, Kpautagi ya ce ya yi imanin cewa matashin ya dace da aikin kuma zai iya haɗa matasa cikin harkokin gwamnati.

Ya kuma nuna kyakkyawan fata cewa ADC za ta iya kayar da gwamnatin Mohammed Bago a zaɓen 2027 saboda tana da goyon bayan al’ummar jihar.

Kpautagi ya ce:

“Za mu gudanar da kamfen ba tare da zage-zage ko ɓata sunan mutane ba. Kamfen ɗinmu zai kasance kan batutuwan da suka shafi al’umma.”

Kara karanta wannan

Kano ta karyata sanya wasu dattawa a auren gata, ta ba limaman Juma'a umarni

Ya yi alkawarin tabbatar da tsaro

Kpautagi ya ce ɗaya daga cikin muhimman manufofin ADC shi ne tabbatar da tsaro, yana mai cewa hakan na cikin alkawuran da jam’iyyar ta ɗauka.

Ya kuma yi alkawarin cewa idan aka zaɓe shi, gwamnatinsa za ta tallafa wa ’yan kasuwa, manoma da matasa.

Alhaji Mamman Musa.
Lokacin da ADC ta ayyana Alhaji Mamman Musa a matsayin dan takarar mataimakin gwamnan Neja Hoto: Musa Abubakar
Source: Facebook

Ya ce za ta mayar da hankali wajen dawo da masana’antu tare da samar da yanayin da zai ba ƙananan sana’o’i damar bunƙasa, kamar yadda tashar Channels tv ta kawo.

ADC na fatan hadakar yan adawa a 2027

A wani labarin, kun ji cewa ADC ta ce har yanzu akwai yiwuwar jam’iyyun adawa su hadu a fitar da dan takara guda wanda zai fafata da shugaban kasa mai ci, Bola Tinubu.

Kakakin jam’iyyar na kasa, Bolaji Abdullahi, ya bayyana haka yayin wata hira, inda ya ce ADC ta yi imanin cewa ‘yan adawa za su fi samun damar kayar da jam’iyyar APC idan suka hada karfi wuri guda.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262