Gowon Ya Fadi yadda Obasanjo Ya Bijire Masa kan Aiki ƙarƙashin Murtala Mohammed

Gowon Ya Fadi yadda Obasanjo Ya Bijire Masa kan Aiki ƙarƙashin Murtala Mohammed

  • Janar Yakubu Gowon ya bayyana yadda Olusegun Obasanjo ya watsi da shawarar da ya ba shi lokacin yakin basasa a Najeriya
  • Gowon ya ce Obasanjo ya ƙi yin aiki ƙarƙashin Murtala Muhammed a lokacin yaƙin saboda batun girman matsayi
  • Ya ce ya tilasta Obasanjo ya amince da umarnin gwamnati, sannan ya yaba masa kan biyayya da kishin ƙasa a lokacin yaƙin

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Abuja - Janar Yakubu Gowon mai ritaya ya bayyana wasu abubuwa da suka faru lokacin yakin basasa.

Gowon ya ce tsohon shugaban ƙasa, Olusegun Obasanjo ya taɓa ƙin yin aiki ƙarƙashin Kanal Murtala Muhammed lokacin yaƙin basasar Najeriya.

Gowon ya sake yin magana kan yakin basasa
Tsohon shugaban soja a Najeriya, Janar Yakubu Gowon. Hoto: Kola SULAIMON.
Source: Getty Images

Gowon ya bayyana hakan ne a cikin littafinsa mai suna “My Life of Duty and Allegiance” wanda aka ƙaddamar a Abuja, cewar Punch.

Kara karanta wannan

Duk da ƙaryata Amurka, an tabbatar da hannun Trump a hallaka jagoran ISIS a Najeriya

Ya ce Obasanjo ya shaida masa kai tsaye cewa ba zai taɓa karɓar umarni daga Murtala ba saboda yana ganin ya fi shi girman matsayi a soja.

Sai dai Gowon ya ce a matsayinsa na babban kwamandan ƙasa, ya dage kan cewa yana da ikon tura jami’ai duk inda gwamnati ke buƙatarsu.

A cewarsa, daga baya Obasanjo ya amince da aikin, inda ya jagoranci Rear Command a Ibadan domin kula da tsaro da kayan tallafi a yankin Yamma.

Gowon ya yaba wa Obasanjo saboda yadda ya gudanar da aikinsa cikin nasara tare da nuna biyayya da kishin ƙasa a lokacin yaƙin basasar Najeriya.

Ya ce Obasanjo ya hana yunƙurin marubuci Wole Soyinka na taimaka wa Kanal Victor Banjo shiga yankin Yamma ta hanyar Benin zuwa Ibadan.

Tsohon shugaban ƙasar ya kuma bayyana yadda ya fara haɗuwa da Obasanjo a Birtaniya a shekarar 1958 lokacin horon jami’an soja na Najeriya.

A cewarsa, Obasanjo ya taimaka masa da kuɗi lokacin da ya isa Landan ba tare da isasshen kuɗin biyan kuɗaɗensa ba a sansanin jami’ai.

Kara karanta wannan

2027: Martanin Kwankwaso ga zargin yana yi wa Tinubu aiki a NDC

Gowon ya ce wannan taimako ne ya sa ya fara kula da Obasanjo tare da zama tamkar “mala’ikan kariya” gare shi har bayan yaƙin basasa.

Ya bayyana Obasanjo a matsayin jami’i mai nutsuwa da hankali, duk da cewa ya ce wasu ƙananan jami’ai sun fi shi saurin fahimta a lokacin.

Ya ce jami’in diflomasiyya Moses Ihonde ne ya aika bayanan zuwa Lagos bayan masu cinikin jirgin sun tuntubi ofishin jakadancin kan farashin canjin kuɗi.

Gowon ya kuma bayyana Murtala Muhammed a matsayin zaɓinsa na farko wajen jagorantar rundunar 2 Division saboda jarumtaka da ƙwazon da yake nunawa.

Sai dai ya ce Murtala yana yawan bari zuciya da fushi su rinjayi tunaninsa, duk da irin ƙwazon da ya nuna a lokacin yaƙin basasa.

Gowon ya fadi dalilin yakin basasa

A baya, an ji cewa Janar Yakubu Gowon ya ce yarjejeniyar Aburi ta rushe ne saboda sabani da Chukwuemeka Ojukwu kan ba gwamnonin sojoji iko.

Gowon ya ce Ojukwu ya so gwamnoni su jagoranci sojoji a yankunansu, amma gwamnati ta ki amincewa saboda ya saba wa doka.

Tsohon shugaban ya ce rashin lafiyarsa da sanarwar da Ojukwu ya fitar sun jawo rushewar yarjejeniyar Aburi tare haddasa yakin basasa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.