Bayan Barazanar da Suka Yi, Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Karin Alawus na 40% ga Ma’aikata
- Bayan barazanar yajin aiki, gwamnatin tarayya ta amince da biyan sabon alawus na musamman ga ma’aikatan gwamnati a Najeriya
- An ce sabon tsarin zai fara aiki daga 1 ga Mayu, 2026 domin rage radadin matsin tattalin arziki da yan Najeriya musamman ma'aikata ke fuskanta
- Shugabar ma’aikatan gwamnatin tarayya ta jaddada muhimmancin tattaunawa da gina amana tsakanin gwamnati da kungiyoyin kwadago
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Abuja, Nigeria - Gwamnatin tarayya ta amince da biyan karin alawus na musamman na kashi 40 cikin 100 ga ma’aikatan gwamnatin tarayya bayan matsin lamba da barazanar yajin aiki daga kungiyoyin kwadago.
Rahotanni sun nuna cewa an cimma matsayar ne bayan wani dogon zama da shugabar ma’aikatan gwamnatin tarayya, Esther Walson-Jack, ta jagoranta ranar Talata a Abuja.

Source: Twitter
Ma'aikata za su samu alawus na 40%
Bussiness Day ta rahoto cewa a yayin taron, Hukumar Kula da Albashi da Kudin Shiga ta Kasa (NSIWC) ta fitar da takardar aiwatar da sabon alawus din.
Wannan lamarin ya kawo karshen kusan shekara biyu na koke-koken ma’aikata kan jinkirin da aka samu wajen daidaita albashi bayan amincewa da sabon mafi karancin albashi N70,000.
Shugabar ma’aikatan gwamnatin tarayya ta jaddada muhimmancin tattaunawa da gina amana tsakanin gwamnati da kungiyoyin kwadago domin kauce wa rikice-rikice da yajin aiki.
Ta ce duk da cewa kungiyoyin kwadago na da ‘yancin gabatar da bukatunsu, dole ne bangarorin gwamnati su samar da damar tattaunawa domin tabbatar da zaman lafiya a wuraren aiki.
Kungiyoyin kwadago sun yaba
Taron ya bai wa Majalisar hadin gwiwar kungiyoyin kwadago (JNPSNC) karkashin Benjamin Uyanto da shugaban NSIWC, Eyo Nta, damar gabatar da korafinsu kafin shugabar ma’aikatan gwamnati ta shiga tsakani domin samar da mafita.
Dukkan bangarorin sun yaba wa Esther Walson-Jack bisa rawar da ta taka wajen warware rikicin, kamar yadda Vangaurd ta ruwaito.
Bayan tattaunawar, an gabatar da jadawalin aiwatar da sabon alawus na kashi 40 cikin 100 ga shugabannin JNPSNC.

Kara karanta wannan
Hajjin 2026: Kasar Saudiyya ta yi gyare gyare, ta tura tallafi ga kasashen Musulmi 27
Yan kwadago sun yi babbar nasara
Sakataren JNPSNC, Olowoyo Gbenga, ya bayyana matakin a matsayin babbar nasara ga ma’aikatan gwamnatin Najeriya musamman a wannan lokaci na matsin tattalin arziki.
A cewarsa, sabon tsarin zai fara aiki daga ranar 1 ga watan Mayun 2026 bayan ma’aikata sun shafe lokaci tun daga watan Yulin 2024 suna jiran aiwatar da tsarin da ya danganci sabon mafi karancin albashi.
Ya kuma bukaci gwamnatocin jihohi su rungumi tsarin domin ma’aikatan jihohi da kananan hukumomi su amfana.

Source: Getty Images
An dakatar da shirin yajin aiki
Olowoyo ya bayyana cewa kungiyar ta riga ta sanya ranar 21 ga watan Mayu domin fara yajin aikin kasa baki daya saboda jinkirin aiwatar da sabon tsarin.
Sai dai ya ce shiga tsakani da ofishin shugabar ma’aikatan gwamnatin tarayya ya taimaka wajen shawo kan matsalar tare da dawo da kwarin gwiwar ma’aikata.
Yan Kwadago sun yi maganar karin albashi
A wani labarin, kun ji cewa kungiyoyin ƙwadago da suka hada da NLC da TUC sun ce za a fara tattaunawa kan sabon mafi ƙarancin albashi a Najeriya a watan Yulin 2026.
Shugaban NLC, Joe Ajaero, ya ce za a fara tattaunawa da wuri ne na da nufin tabbatar da cewa an kauce wa tsaiko da aka saba samu a tattaunawar albashi a baya.
Ya buƙaci ma’aikata da su haɗa kai domin neman albashi mai ma’ana.wanda ya dace da halin da tattalin arzikin ƙasar ke ciki a halin yanzu.
Asali: Legit.ng

