Majalisar Dinkin Duniya Ta Sa Baki kan Harin Sojojin Sama da Ya Kashe Farar Hula a Zamfara

Majalisar Dinkin Duniya Ta Sa Baki kan Harin Sojojin Sama da Ya Kashe Farar Hula a Zamfara

  • Ana ci gaba da magana kan harin sojojin sama da ake zargin ya jawo asarar rayukan farar hula da dama a jihar Zamfara
  • Majalisar dinkin duniya ta yi tsokaci kan harin tare da wani makamancinsa da sojojin Chadi suka kai a Tafkin Chadi
  • Babban jami'in kare hakkin dan Adam na Majalisar dinkin duniya ya bukaci a gudanar da bincike mai zaman kansa cikin gaggawa

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

​​​​​​​​​​Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

FCT, Abuja - Babban jami’in kare haƙƙin ɗan Adam na Majalisar dinkin duniya, Volker Turk, ya yi magana kan hare-haren da sojojin sama suka kai a Najeriya da Chadi.

Volker Turk ya buƙaci a gudanar da bincike mai zaman kansa kan rahotannin da ke cewa hare-haren sama daban-daban da dakarun Najeriya da na Chadi suka kai a Arewacin Najeriya sun kashe farar hula fiye da 100.

Kara karanta wannan

"Babu hujja," Sojojin Najeriya sun yi magana kan zargin kashe fiye da mutane 100 a Zamfara

Majalisar dinkin duniya ta nuna damuwa kan harin Zamfara
Shugaban kwamitin kare hakkin dan Adam na Majalisar dinkin duniya, Volker Turk Hoto: @volker_turk
Source: Twitter

Volker Turk ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da ya fitar a shafin X a ranar Laraba, 13 ga watan Mayun 2026.

Ana fargabar kashe fararen hula a Zamfara

A cewar ƙungiyar Amnesty International an kashe akalla mutane 100 a harin da sojojin suka kai a kasuwar Tumfa da ke jihar Zamfara.

Yayin da take ambato shaidun gani da ido, Amnesty ta ce da dama daga cikin waɗanda aka kashe mata ne da kananan yara, sannan ta buƙaci hukumomi da su yi bincike kan harin.

Rahotanni sun bayyana cewa luguden wutar sojojin Chadi ya kashe masuntan Najeriya da dama da ke aiki a tsibiran da ke ƙarƙashin ikon Boko Haram, inda ake tilasta wa farar hula biyan haraji ga ƙungiyar 'yan ta'addan.

Me majalisar dinkin duniya ta ce kan harin?

“Na firgita da rahotannin cewa hare-haren saman da sojojin Najeriya suka kai a wata kasuwa a jihar Zamfara sun kashe aƙalla farar hula 100 ranar 10 ga Mayu tare da jikkata wasu da dama."

Kara karanta wannan

Ana fargabar harin sojojin sama ya kashe kusan mutane 100 a Zamfara

- Volker Turk

Ya ce ya kuma kasance “cikin fargaba da baƙin ciki” sakamakon rahotannin yawan asarar rayukan farar hula a hare-haren da jiragen yaƙin kasar Chadi suka kai tun ranar Juma’a a sansanonin Boko Haram da ke kan wasu tsibiran daji a yankin tafkin Chadi.

"Yana da matuƙar muhimmanci hukumomin Najeriya da na Chadi su gudanar da bincike cikin gaggawa, dalla-dalla, mai zaman kansa kuma ba tare da nuna son kai ba kan waɗannan abubuwa masu tada hankali."

- Volker Turk

Ana fargabar kashe fararen hula a Zamfara
Volker Turk na jawabi a wajen wani taro Hoto: @volker_turk
Source: Twitter

Majalisar dinkin duniya ta bukaci a yi bincike

Ya ƙara da cewa dole ne dakarun sojojin biyu su dauki duk wani matakin kariya da za a iya don kauce wa cutar da farar hula.

“Dole ne a gudanar da ayyukansu na soja, ciki har da yaƙi da Boko Haram da abin da ake kira ‘Islamic State West Africa Province’ (ISWAP) cikin cikakken bin dokokin jin ƙai na ƙasa da ƙasa da kuma dokokin haƙƙin ɗan adam na ƙasa da ƙasa."

Kara karanta wannan

Tashin hankali: An kashe mutane 100, an raba mutum 98,000 da gidajensu a Taraba

"Kada farar hula da ababen amfanin farar hula su taɓa zama abubuwan kai hari."

- Volker Turk

Gwamnatin Zamfara ta magantu kan harin sojoji

A wani labarin kuma, kun ji cewa Gwamnatin jihar Zamfara ta yi martani kan harin da sojojin sama suka kai a wata kasuwa a jihar.

Gwamnatin jihar Zamfara ta ce yankin da aka kai harin sanannen maboyar ‘yan bindiga ne da jami’an tsaro ke bibiyarsu.

Mai ba gwamnan Zamfara shawara kan harkokin tsaro, Ahmed Danmanga, ya ce gwamnatin jihar ba ta san akwai kasuwa a yankin ba.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng