Gwamnatin Zamfara Ta Magantu da Ake Zargin Harin Jirgi Ya Kashe Yan Kasuwa 100

Gwamnatin Zamfara Ta Magantu da Ake Zargin Harin Jirgi Ya Kashe Yan Kasuwa 100

  • An samu ce-ce-ku-ce bayan harin saman da rundunar sojin saman Najeriya ta kai kasuwar Tumfa a jihar Zamfara
  • Majiyoyi suka ce mazauna yankunan sun tabbatar da cewa kusan mutum 100 sun mutu sakamakon harin jirgin da aka kai
  • Sun bayyana cewa mata da yara sun fi yawa cikin wadanda suka mutu, yayin da gwamnati ta dage cewa yankin maboyar ‘yan bindiga ne

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Zurmi, Zamfara - Rikici ya biyo bayan harin saman da aka kai kasuwar Tumfa da ke karamar hukumar Zurmi a Zamfara.

An tabbatar da cewa mazauna yankin sun bayyana cewa mutane da dama sun mutu yayin harin.

Ana zargin jirgin saman Najeriya ya babbake yan kasuwa
Taswirar jihar Zamfara da yan ta'adda ke kai hare-hare a yankuna da dama. Hoto: Legit.
Source: Original

Ana zargin rundunar sojin saman Najeriya da kai harin ranar Lahadi 9 ga watan Mayun 2026 yayin da kasuwar ke cike da masu saye da sayarwa, cewar Leadership.

Kara karanta wannan

Ana fargabar harin sojojin sama ya kashe kusan mutane 100 a Zamfara

Abin da mazauna Zamfara ke cewa

Wani mazaunin yankin da ya yi magana da harshen Hausa ta wayar tarho ya ce harin ya afku ba tare da gargadi ba.

Ya bayyana cewa mafi yawan wadanda suka mutu mata ne, domin su ne suka fi yawa cikin ‘yan kasuwar da suka halarta.

Mazaunin ya kara da cewa an kai wadanda suka jikkata zuwa manyan asibitocin Zurmi da Kaura Namoda domin samun kulawa ta musamman.

Gwamnatin Zamfara ta magantu kan kisan wasu yan kasuwa
Gwamna Dauda Lawal Dare na jihar Zamfara. Hoto: Dauda Lawal.
Source: Twitter

Martanin gwamnatin Zamfara kan 'harin'

A gefe guda, gwamnatin Zamfara ta ce yankin da aka kai harin sanannen maboyar ‘yan bindiga ne da jami’an tsaro ke bibiyarsu.

Mai ba gwamnan Zamfara shawara kan harkokin tsaro, Ahmed Danmanga, ya ce gwamnatin jihar ba ta san akwai kasuwa a yankin ba.

Shugaban karamar hukumar Zurmi, Hon. Samaila Hussaini Moriki, ya ce ana gudanar da bincike domin gano hakikanin abin da ya faru a yankin.

Rahotanni sun nuna cewa kauyen Tumfa na daga cikin wuraren da ake fama da hare-haren ‘yan bindiga da rikice-rikicen tsaro a Zamfara.

Kara karanta wannan

"Yara na 3 sun mutu," Magidanci ya sabawa bayanin sojoji kan kuskuren jefa bam a Neja

Rahoton ya bayyana cewa wannan ne karo na biyu cikin wata guda da harin sama ya afkawa kasuwa mai cike da jama’a.

Amnesty Int'l ta yi magana kan harin

Kungiyar Amnesty International ta ce akalla fararen hula 100 ne suka mutu a harin, tare da bukatar gudanar da bincike cikin gaggawa.

Kungiyar ta bayyana cewa mata da yara mata na daga cikin wadanda suka mutu, yayin da wasu da dama ke kwance a asibitoci, cewar Daily Post.

Amnesty International ta ce jiragen yaki sun fara shawagi kan yankin kafin daga bisani su dawo suka kai harin kan kasuwar Tumfa.

Kungiyar kare hakkin dan Adam ta zargi jami’an tsaro da nuna rashin kula da rayukan fararen hula yayin yakar ‘yan bindiga da masu tada kayar baya.

Har zuwa lokacin hada wannan rahoto, rundunar sojin Najeriya ba ta fitar da wata sanarwa a hukumance kan lamarin da ya faru ba.

Sojoji sun kashe jagoran yan ta'adda

An ji cewa dakarun sojojin sama na Najeriya sun kai hare-hare kan wani wuri da 'yan ta'adda ke gudanar da taro a jihar Zamfara.

Kara karanta wannan

Dan damfara ya sace wa mahajjaciya 'yar Najeriya daloli a Madina

Sojojin saman sun samu nasarar hallaka 'yan ta'adda da dama ciki har da jagororinsu bayan sun yi masu ruwan wuta.

A cewar sanarwar da aka fitar, an kai hare-haren ne bayan samun bayanan sirri wadanda suka tabbatar da cewa jagororin 'yan ta'addan na gudanar da taro.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.