Mutuwa Ta Sake Girgiza Najeriya, Tsohon Antoni Janar Ya Riga Mu Gidan Gaskiya
- Tsohon Antoni-Janar kuma kwamishinan shari'a na Jihar Legas, Farfesa Alfred Kasunmu, ya riga mu gidan gaskiya
- Kasunmu ya kasance Babban Lauyan Najeriya (SAN) kuma tsohon shugaban tsangsyar koyar da harkokin doks na Jami’ar Legas
- Marigayin ya kuma yi aiki a matsayin Antoni-Janar na jihar Legas daga daga shekarar 1975 zuwa 1978
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Lagos, Nigeria - Tsohon Antoni-Janar na Jihar Legas, Farfesa Alfred Kasunmu, ya rasu a safiyar Lahadi, 9 ga Agusta, 2026.
Kasunmu, wanda yake Babban Lauyan Najeriya (SAN), ya rasu cikin kwanciyar hankali, kamar yadda iyalansa suka bayyana a wata sanarwa.

Source: Twitter
The Cable ta rahoto cewa iyaalansa sun bayyana marigayin a matsayin fitaccen malami, mai ba da shawara da kuma uban iyali, wanda ya bar tarihi mai cike da hikima, mutunci da hidima da suka zama abin koyi ga al’ummomi masu zuwa.
Sanarwar ta ce:
“Farfesa Kasunmu ba uban iyalinmu ne da muke matukar kauna kawai ba, ya kasance fitaccen malami, mai ba da shawara kuma Babban Lauya a Najeriya."
Ya sadaukar da rayuwarsa ga shari’a
Iyalin sun ce Kasunmu ya taimaki rayuwar mutane da dama ta hanyar sadaukar da kansa ga fannin shari’a, ilimi da kuma jin kai.
Sun bayyana cewa za a sanar da cikakken tsarin jana’izar daga baya, yayin da aka shirya zaman makoki a gidansa ranar Asabar, 15 ga Agusta, da Lahadi, 16 ga Agusta, daga karfe 1:00 na rana zuwa 7:00 na yamma.
Iyalin sun kuma bukaci jama’a da su yi addu’a a lokacin makokin, suna mai cewa suna samun kwanciyar hankali ne daga tunawa da irin rayuwar da marigayin ya yi.
Kasunmu ya fara aikin lauya a 1964
Marigayi Kasunmu ya zama cikakken lauya a Najeriya a 1964, sannan a wannan shekarar ya shiga Faculty of Law ta Jami’ar Ife, wadda yanzu ake kira Jami'sr Obafemi Awolowo, a matsayin daya daga cikin malaman farko na jami’ar.
A shekarar 1971, ya koma Jami’ar Legas inda ya zama babban malami. Shekaru biyu bayan haka, a 1973, aka nada shi Farfesa a fannin shari’a, sannan ya rike mukamin shugaban tsangsya daga 1973 zuwa 1975.

Source: Original
Ya zama Antoni-Janar na Legas
Marigayi Kasunmu ya yi aiki a matsayin Antoni-Janar na Jihar Legas daga shekarar 1975 zuwa 1978, kamar yadda Punch ta ruwaito.
Bayan ya kammala wannan aiki, ya koma aikin lauya mai zaman kansa, inda ya kafa kamfanin lauyoyi na Prof. A.B. Kasunmu Chambers. Baya ga aikin lauya da koyarwa, Kasunmu ya kasance fitaccen marubucin littattafan shari’a.
Tsohon daraktan Majalisar tarayya ya rasu
Kun ji cewa tsohon Darakta Janar kuma Magatakardan Majalisar Tarayya na farko, Dr. Adamu Mohammed Fika, ya riga mu gidan gaskiya.
Marigayin, wanda ke rike da sarautar Zarma Kura na Fika, ya riga mu gidan gaskiya ne a wani asibiti da ke babban birnin tarayyya, Abuja.
Rahotanni sun nuna cewa 'yan uwa, abokan aiki da sauran masu alaka da marigayi Dr. Muhammad Fila sun fara bayyana alhininsu kan rasuwarsa tare da mika sakon ta'aziyya.
Asali: Legit.ng

