Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa da Yan Uwan Mataimakin Gwamna a Jihar Sakkwato
- 'Yan bindiga sun shiga yankin da mataimakin gwamnan jihar Sakkwato ya fito, sun yi awon gaba da mutane takwas jiya Alhamis
- Rahotanni sun nuna cewa daga cikin wadanda suka fada hannun maharan har da 'yan uwan mataimakin gwamnan
- Mazauna yankin sun yi kira ga gwamnati da ta taimaka ta kawo masu dauki don ceto su daga matsalar tsaron da suke fama da ita
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Sokoto, Nigeria - Wasu ’yan bindiga ne sun yi garkuwa da mutane takwas a kauyen Garin Idi da ke karamar hukumar Sabon Birni a jihar Sokoto.
Rahotanni sun nuna cewa wasu daga cikin wadanda suka fada hannun 'yan bindigar suna da alaka da mataimakin gwamnan jihar ta Sakkwato, Idris Mohammed Gobir.

Source: Original
Yadda harin ya faru a Sokoto
Majiyoyi sun shaidawa Daily Trust cewa maharan dauke da mugayen bindigogi sun kai harin ne da misalin karfe 1:00 na daren ranar Alhamis.
Daga isarsu garin, 'yan bindigar sun bude wuta kan mai uwa da wabi, wanda ya tilasta mazauna kauyen tserewa zuwa daji domin tsira da rayukansu.
An ce ’yan bindigar sun shafe kusan awa biyu suna cin karensu babu babbaka a kauyen ba tare da wani daukin jami’an tsaro ba.
Wani mazaunin yankin ya ce:
“Ban taba jin harbin bindiga mai tsanani irin na jiya ba. Yanzu idan sun zo muna tsoro, amma idan sun tafi sai mu samu sauki saboda mun saba da hakan."
An sace yan uwan mataimakin gwamna
Wata majiya da ta nemi a sakaya sunanta ta ce maharan sun zo ne a kan babura kusan takwas, inda suka tattara mutane kusan 30, galibi mata da yara, kafin daga bisani su saki wasu su tafi da mutane takwas.
Ta ce daga cikin wadanda aka sace, uku maza ne, biyar kuma mata ne, amma majiyar ta kara da cewa maharn sun saki wasu yara da wasu mutane saboda rashin isasshen wuri a kan baburan su.
An ce yawancin wadanda yan bindigar suka tafi da su zuwa cikin daji, ’yan uwan mataimakin gwamnan ne, kamar yadda Leadership ta ruwaito.
Mutane sun aika sako ga gwamnati
Mazauna yankin sun yi kira ga gwamnati, musamman mataimakin gwamna, da ya dauki matakin gaggawa domin magance matsalar tsaro da ke addabar yankin.
Wani mazaunin garin ya ce:
"Muna rokon sa ya dubi halin da muke ciki. A matsayin dansu kuma mataimakin gwamna, abin takaici ne yadda ake barin mu cikin wannan hali duk da kasancewarmu ’yan uwansa.”

Source: Facebook
Sun nuna damuwa cewa duk da alakar da suke da ita da mataimakin gwamna, har yanzu ana ci gaba da kai hare-hare a yankin ba tare da daukar matakin gaggawa ba.
Yunkurin jin ta bakin kakakin rundunar ’yan sandan jihar Sokoto, DSP Ahmad Rufai, bai yi nasara ba har zuwa lokacin hada wannan rahoto.
Yan bindiga sun sace bayin Allah a Sokoto
A wani labarin, kun ji cewa wasu da ake zargin 'yan bindiga ne sun kai hari garin Achida da ke Ƙaramar Hukumar Wurno a Jihar Sokoto.
Bayanai daga yankin sun nuna cewa maharan sun kashe mutane biyu tare da yin garkuwa da aƙalla mutane 25 a yayin harin.
Wani mazaunin garin, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya ce maharan sun fara farmakar wurin jami'an sa-kai ne da ke gefan garin.
Asali: Legit.ng


