Bukatar Hukumar DSS ga Babbar Kotu kan ci Gaba da Shari’ar El Rufai a Abuja
- Hukumar DSS ta tura bukata ta musamman ga kotu kan ci gaba da shari'ar da ake yi game da zargin Malam Nasir El-Rufai
- DSS ta nemi kotu ta ɓoye sunayen shaidu a shari’ar Nasir El-Rufai, tana mai cewa hakan na da muhimmanci domin kare lafiyarsu
- El-Rufai ya musanta tuhume-tuhume guda biyar da ake yi masa kan zargin sauraron tattaunawar waya ba tare da izini ba
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.
Abuja - Hukumar tsaro ta farin kaya, DSS ta tura bukata ta musamman ga babbar kotun tarayya kan shari'ar tsohon gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufai.
An gurfanar da tsohon gwamnan Kaduna a gaban kotu kan tuhume-tuhume guda biyar da suka shafi zargin samun damar leken asirin tattaunawar waya ba tare da izini ba.

Source: Twitter
Bukatar hukumar DSS ga kotu a Abuja
Hukumar DSS ta bukaci kotun da ke Abuja ta ba ta damar ɓoye sunayen wasu shaidu biyu da ake sa ran za su bayar da shaida a shari’ar Nasir El-Rufai, cewar TheCable.
Bayan karanta masa tuhume-tuhumen, El-Rufai ya musanta dukkan laifukan da ake tuhumarsa da su inda ya ke zargin akwai kullalliyar kan zarge-zargen da ake yi masa.
Lauyan DSS ya roki kotu ta ba da damar shaidun su bayar da shaida a ɓoye saboda dalilan tsaro da kare lafiyarsu duba da yadda shari'ar ke da girma a yanzu.

Source: Twitter
Lauyan El-Rufai ya yi fatali da bukatar DSS
Sai dai lauyan El-Rufai ya yi adawa da wannan bukata inda ya ke ganin an saba dokar kasar Najeriya wanda hakan ka iya jawo matsala a shari'ar da ake yi.
Lauyan ya bayyana cewa kundin tsarin mulki ya ba wanda ake tuhuma damar sanin shaidun da ke tuhumarsa wanda zai iya ba shi damar samun wasu hujjoji.
Ya kuma ce DSS ba ta gabatar da wata hujja da ke nuna cewa El-Rufai na iya barazana ga shaidun ba.
Bangaren tsaro ya kuma ƙi amincewa da bukatar a gabatar da cikakken bayanan shari’ar ga wanda ake tuhuma domin shirin kare kansa.
Haka kuma Malam Nasir El-Rufai ya shigar da bukatar beli, wanda DSS ta ce ba za ta hana shi ba.
A ƙarshe, kotu ta ɗage sauraron karar zuwa ranakun 18, 19 da 20 na watan Mayu domin ci gaba da shari’ar, cewar rahoton Punch.
El-Rufai ya zargi ana kulla masa makarkashiya
A baya, mun ba ku labarin cewa tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir Ahmad El-Rufai, ya nuna damuwa kan sabon shirin da ya yi zargin ana kullawa a kansa.
Tsohon gwamnan Kaduna ya nuna cewa ana yin wata kulla-kulla domin ganin an ci gaba da tsare shi a hannun hukumomi saboda wasu bukatun gwamnati mai ci.
Nasir El-Rufai ya yi zargin cewa ana kokarin alakanta da wasu laifuffuka domin ganin ya gaza samun beli lamarin da ke kara jawo maganganu da zargin akwai siyasa a ciki.
Asali: Legit.ng

