Hukumar DSS
An kashe ’yan bindiga 24 bayan jami’an tsaro sun dakile yunkurin yin garkuwa da mazauna Gidan Bawa a Bakori, Jihar Katsina, tare da kwato shanu 19.
Gwamna Seyi Makinde ya zaɓi tsohon Darakta-Janar na DSS, Lawal Daura, a matsayin abokin takararsa na jam'iyyar APM a zaɓen shugaban ƙasa na shekarar 2027.
Dan Etete ya kalubalanci zargin cewa Janar Sani Abacha ya mutu yayin saduwa da wata mata, yana neman hujjoji da takardun da za su tabbatar da labarin.
Lawal Musa Daura ya sauya-sheka watanni 7 da ayyana neman takarar gwamna a ADC. Wannan karo ya tattara jama'ansa zuwa jam'iyyar APM mai alamar rogo.
A labarin nan, za a ji yadda gaskiya ta yi halinta bayan bincike ya gano cewa wani matashi dan jihar Katsina ba shi da hannu a garkuwa da daliban Oyo.
DSS ta gurfanar da tsohon jami'inta Nwaogu Ezeakolam kan zargin shiga IPOB, tallafa mata da yada sakonnin goyon baya, yayin da kotu ta tsare shi a Kuje.
Tsohon kyaftin din ruwa Erasmus Victor ya ce ya san zargin shirin juyin mulki amma ya gargadi Kanal Ma’aji ya dakatar da shi, yana musanta goyon bayan shirin.
Hukumar DSS ta yi gargaɗin cewa Boko Haram na shirin kai manyan hare-hare a Michika ta Adamawa da Askira-Uba ta Borno bayan rugujewar yarjejeniyar tsagaita wuta.
DSS ta gurfanar da mutum biyar da ake zargin mambobin Ansaru ne kan sace ɗalibai da malamai a Oyo da kashe mutum biyu, yayin da kotu ta ce a tsare su.
Hukumar DSS
Samu kari