Yaki da cin hanci a Najeriya
Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa ta EFCC ta bayyana cewa a halin yanzu tana gudanar da bincike kan jihohi kusan 18 bisa zargin almundahanar kuɗaɗen gwamnati.
Halima Shehu ta roƙi Tinubu ya umarci EFCC ta fitar da rahoton binciken da ta yi, tana cewa hakan zai wanke sunanta daga zarge-zargen da aka yi mata.
Ofishin Kasafin Kudi ya ce hukumar bogi ta PFIPC ta samo asali tun mulkin marigayi Muhammadu Buhari, tare da jaddada cewa ba a taba sakin ko sisi gare ta ba.
Femi Gbajabiamila, wanda shi ne shugaban ma'aikatan fadar shugaban kasa, ya shigar da kara a kotun Abuja kan Adeniyi Adeyemi bisa zargin bata masa suna.
Ƙungiyar SERAP ta kai INEC kotu tana neman ta binciki zargin cewa gwamnonin APC sun karkatar da kusan N800bn daga kudaden FAAC domin yakin neman zaben 2027.
Hukumar EFCC ta bayyana yadda ake shigar da koke kan zargin damfara ta shafinta, tare da gargadin cewa ƙorafin ƙarya laifi ne mai hukunci mai tsanani.
Babbar kotun tarayya mai zama a Abuja ta sauya ranar yanke hukunci kan shari'ar da EFCC ta nemi a karɓe kadarori 57 da ke da alaka da Abubakar Malami.
Shari'ar tsohon Ministan Sufurin Jiragen Sama, Sanata Hadi Sirika, ta dauki sabon salo bayan kotu ta saurari sakon murya da aka ce nasa ne yayin zamanta.
Babbar kotun Abuja ta amince da bukatar tsare tsohon shugaban CCT na kasa, Danladi Umar a gidan yari bayan gurfanar da shi kan zargin karbar rashawa.
Yaki da cin hanci a Najeriya
Samu kari