Kasar Musulunci Ta Iran Ta Yi Sabon Zubi a Rundunar Sojojinta ana tsakiyar Yaki da Amurka

Kasar Musulunci Ta Iran Ta Yi Sabon Zubi a Rundunar Sojojinta ana tsakiyar Yaki da Amurka

  • Jagoran addinin Iran, Ayatollah Mojtaba Khamenei ya nada manyan kwamandojin soji shida domin inganta ayyukan rundunar kasar
  • Ali Abdollahi ya zama Shugaban Hafsan Hafsoshin Sojojin Iran yayin da Ahmad Vahidi ya zama sabon kwamandan IRGC
  • Haka zalika Khamenei na sa ran Mohsen Rezaee zai taka muhimmiyar rawa a tattaunawar Iran da kasashen waje

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Islamic Republic of Iran - Jagoran Iran kuma kwamandan askarawan kasar, Mojtaba Hosseini Khamenei, ya sanar da nada manyan kwamandojin soji shida.

Kwamandojin za su aiki ne a wasu muhimman mukamai a rundunar sojin kasar, Rundunar Kare Juyin Juya Halin Musulunci (IRGC) da kuma rundunar Basij.

Khmenei.
Jagoran addinin Jamhuriyar Musulunci ta Iran, Mojtaba Khamenei Hoto: SOPA Images
Source: Twitter

Tashar Al-Jazeera ta rahoto cewa Khamenei ya sanar da sababbin nade-naden ne ta shafinsa na Telegram.

Ya bayyana cewa ya rattaba hannu kan umarnin nada manyan jami’an soji a matsayin wani bangare na sauya tsarin jagoranci a bangaren tsaro na Iran.

Kara karanta wannan

Iran ta ƙara shiri, Mojtaba Khamenei ya yi wani muhimmin gyara ana cikin yaƙi da Amurka

Khamenei ya nada sababbin kwamandoji

Mojtaba ya nada Manjo Janar Ali Abdollahi a matsayin Babban Hafsan Hafsoshin Sojojin Iran, yayin da Birgediya Janar Kioumars Heydari ya zama mataimakinsa.

Haka kuma, Ahmad Vahidi, wanda aka daga masa matsayi zuwa Manjo Janar, ya zama sabon kwamandan Rundunar Kare Juyin Juya Halin Musulunci ta Iran, wato IRGC.

An nada Mostafa Izadi a matsayin mataimakin Vahidi a shugabancin rundunar yayin da bangaren rundunar ruwa ta IRGC kuwa, aka nada Rear Admiral Ali Ozmaei a matsayin kwamanda.

Haka kuma, Hossein Taeb ya samu mukamin shugaban rundunar Basij, wata rundunar sa-kai mai matukar muhimmanci a tsarin tsaron Iran.

Sabbin nade-naden sun shafi wasu daga cikin manyan cibiyoyin tsaro da soji na Iran, lamarin da ke nuna yiwuwar samun sauyi a tsarin jagorancin bangaren tsaron kasar.

Rezaee na iya jagorantar tattaunawa

A wani bangaren, nadin Mohsen Rezaee a matsayin babban jami’in tsaron Iran na iya sauya salon da kasar ke bi wajen gudanar da tattaunawa da sauran kasashe.

Kara karanta wannan

Mutuwa ta sake girgiza Najeriya, tsohon antoni janar ya riga mu gidan gaskiya

Muhanad Seloom, mataimakin farfesa kan harkokin siyasar kasa da kasa da tsaro a Doha Institute for Graduate Studies, ya ce Rezaee na iya taka muhimmiyar rawa a duk wata tattaunawa da za a yi nan gaba.

Sojojin Iran.
Dakarun rundunar sojojin kasar Iran a cikin shirin ko ta kwana Hoto: Anadolu
Source: Getty Images

Ya bayyana cewa Rezaee tsohon kwamandan IRGC ne kuma mutum ne da Khamenei ya zaba da kansa, kamar yadda rahoton The Times of Israel ya nuna.

Seloom ya ce wasu raho tanni daga Iran na nuna cewa nadin Rezaee na iya kasancewa wani mataki na daidaita karuwar tasirin Kakakin Majalisar Iran kuma babban mai shiga tattaunawar kasar, Mohammad Bagher Ghalibaf.

Iran ta naɗa shugaban Majalisar tsaro

A wani labarin, kun ji cewa jagoran addini na kasar Iran, Ayatollah Mojtaba Khamenei ya nada Mohsen Rezaee da Mohammed Bagher Zolghadr manyan mukamai

Rezaee ya zama wakilin Mojtaba Khamenei a Majalisar Tsaron Jamhuriyar Musulunci ta Iran a daidai lokacin da ake yaki da Amurka.

Rezaee ya jagoranci IRGC daga shekarar 1981 zuwa 1997, lokacin da rundunar ke kara karfafa matsayinta a tsarin tsaro da siyasar Iran.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262