Yunkurin Tsige Gwamna Ya Jefa Shugaba Tinubu a Matsala, An Yi Masa Barazana

Yunkurin Tsige Gwamna Ya Jefa Shugaba Tinubu a Matsala, An Yi Masa Barazana

  • Ƴan kalibar Ijaw sun yi barazanar ɗaukar matakin da zai ba Shugaban Kasa, Bola Tinubu mamaki idan ya sake aka tsige Gwamna SImi Fubara
  • Wata kungiyar ƴan Ijaw, mai rajin kare al'adu ta bayyana cewa da sanin Tinubu ne Wike ya ke abin da ya ga dama a rikicin siyasar jihar Ribas
  • A cewar ƴan kabilar, kotu ƴar amshin shatar Wike ce shiyasa aka yanke hukunci daidai da yadda yake so da Mai girma Fubara ya yi kara a kotu

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Rivers - Kalaman Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Nyesom Wike cewa ba abin da zai faru idan aka tsige Gwamna Siminalayi Fubara na jihar Ribas sun tayar da ƙura.

Supreme Egbesu Assembly (SEA), wata ƙungiyar ƴan kabilar Ijaw, ta yi barazanar cewa za ta "ba Shugaba Bola Tinubu mamaki a lokacin da ya dace" idan aka tsige gwamnan.

Kara karanta wannan

Bayan 'wulakacin' da aka masa, gwamna ya aika wasiƙa ga Majalisar Dokoki

Fubara, Wike da Tinubu.
Kungiyar Ijaw ta yi barazanar ba Tinubu mamaki idan aka tsige Gwamna Fubara Hoto: Sir Siminalayi Fubara, Nyesom Wike
Asali: Facebook

Abubuwan da ke faruwa a Ribas

Wannan dai na zuwa ne bayan rikicin siyasar jihar Ribas ya kara dawowa ɗanye tun bayan hukuncin kotun kolin Najeriya, kamar yadda Vanguard ta tattaro.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Haka nan kuma a ranar Laraba da ta gabata, ƴan Majalisar Dokoki 27 na tsagin Wike, waɗanda kotun koli ta tabbatar da sahihancinsu, suka hana Fubara shiga zauren Majalisa.

Lamarin dai ya faru ne a lokacin da Gwamna Fubara ya isa Majalisar da nufin sake gabatar da kasafin kudin 2025 kamar yadda kotun ƙoli ta umarta.

Kwatsam sai aka ji ministan Abuja, Wike na cewa idan Fubara ya aikata laifin da ya cancanta a tsige shi, babu abin da zai faru don ƴan Majalisa sun tunbuke shi.

Kungiyar SEA ta caccaki Wike da Tinubu

Shugaban SEA, Werinipre Digifa, ya yi Allah-wadai da kalaman Wike, yana mai zargin cewa yana nuna girman kai da rashin hankali a kan al’ummar Ijaw.

Kara karanta wannan

Sanata ya watsawa matasa kasa a ido, ya ki amincewa ya kara da Tinubu a 2027

A cewarsa:

"Tinubu ne ke da alhakin wannan girman kai da rashin da’a da Wike ke nunawa a kan mutanen kabilar Ijaw.
"Wike ya riga ya san yadda hukuncin kotun koli zai kasance kafin a yanke shi, kuma haka ya faru daidai da yadda yake so. Wannan ya tabbatar da cewa Najeriya ƙasa ce da ba ta da tsarin doka da oda."
Gwamna Fubara.
Yan kabilar Ijaw sun ɗauki zafi kan kalaman Wike na tsige Gwamna Fubara Hoto: Sir Siminalayi Fubara
Asali: Facebook

Mutanen Ijawa sun yi wa Tinubu barazana

Digifa ya ce mutanen Ijaw ba su da dabi'ar tada rikici, amma za su fuskanci lamarin cikin lalama da kuma dabaru masu kyau.

"Muna lura da irin cin mutuncin da ake wa gwamnan jihar Rivers da kuma kalaman batanci da ake yi wa mutanen ƙabilar Ijaw. Mutanen Neja Delta suna da fahimta.
"Kuma idan matsala ta taso, manya ba su gaggauta shiga. A al’adar Afirka, ana cewa ‘mahaukata biyu ba lokaci guda suka haukace ba'. Don haka mu muna lura da abubuwan da ke faruwa."

Kara karanta wannan

Tinubu ya fadi aikin da ya yi da aka gaza lokacin Buhari, Jonathan, 'Yar'adua

Duk da haka, kungiyar ta bayyana cewa ba za ta dauki matakin tashin hankali ba, amma za ta dauki matakan da suka dace a siyasance domin kare mutuncin mutanen Ijaw.

Shugaba Tinubu ya bukaci a bi umarnin doka

A baya kun ji cewa, Bola Tinubu ya buƙaci shugabannin yankin Kudu maso Kudu su tabbatar da an bi hukuncin kotun ƙoli domin warware rikicin jihar Ribas.

Shugaban ƙasar ya ba da wannan shawara ne yayin wata ganawa da shugabannin yankin Neja Delta karkashin kungiyar PANDEF a Aso Rock da ke Abuja.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen hausa na legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262