Jigon PDP Kuma Tsohon Kakakinta Zai Kwana a Gidan Kaso Bayan Gwamnatin APC Ta Zargeshi da Laifi 1

Jigon PDP Kuma Tsohon Kakakinta Zai Kwana a Gidan Kaso Bayan Gwamnatin APC Ta Zargeshi da Laifi 1

  • Kotun Majistare a birnin Abakaliki da ke jihar Ebonyi ta tsare jigon PDP a gidan kaso kan zargin bata suna da karya
  • Ana zargin Chika Nwoba da aikata laifuka guda uku da suka hada da barazanar kisa da bata suna da kuma ba da bayanan karya
  • An gurfanar da Chika ne wanda shi ne tsohon kakakin jam’iyyar a jihar a yau Talata 13 ga watan Faburairu kan zarge-zargen

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Ebonyi – Jigon jam’iyyar PDP mai adawa a jihar Ebonyi ya shiga matsala bayan tsare shi da aka yi a gidan kaso.

Ana zargin Chika Nwoba da aikata laifuka guda uku da suka hada da barazanar kisa da bata suna da kuma ba da bayanan karya.

Kara karanta wannan

Innalillahi: Mahara sun hallaka jami'an 'yan sanda 2 da sace fiye da 40 a sabon hari a Zamfara

Jigon PDP zai kwana a gidan yari bayan APC ta maka shi a kotu
Jigon PDP, Chika Nwoba ana zarginsa da bata suna da kuma karya a Ebonyi. Hoto: Francis Nwifuru.
Asali: Facebook

Mene ake zargin jigon PDP?

Kotun Magistare da ke birnin Abakaliki a jihar ita ta umarci tsare Chika a gidan gyaran hali bayan gurfanar da shi.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

An gurfanar da Chika ne wanda shi ne tsohon kakakin jam’iyyar a jihar a yau Talata 13 ga watan Faburairu kan zarge-zargen.

Premium Times ta tabbata da cewa an kama Chika ne tun a ranar Lahadi 11 ga watan Faburairu bayan korafin da aka shigar.

Kwamishinan kasuwanci da masana’antu a jihar, Oguzor Offia-Nwali shi ya gabatar da korafi kan Chika a ofishin ‘yan sanda.

Nwali ya zargi Chika da wallafa wasu bayanai a shafin Facebook inda ya ke bata masa suna da cewa ya karkatar da wasu kudaden jihar.

Martanin lauyoyin a shari'ar

Lauyan wanda ake zargi, C N Ufufu ya nemi kotun ta ba da belin wanda ya ke karewa bayan karanto laifukan.

Kara karanta wannan

Hukumar Hisbah a Kano ta kama fitacciyar jarumar TikTok, Murja Kunya

Lauyan ya ce laifin da ya aikata ya cancanci beli inda ya ce masu karar ba su samu amincewa daga kwamishinan shari’a a jihar ba.

Mai Shari’a, Lilian Ogodo ta umarci tsare shi a gidan kaso inda ta ce inda ya dace a gudanar da shari’ar ita ce babbar kotun jihar, cewar Daily Post.

An cafke mata da kisan kai a Legas

Kun ji cewa, rundunar ‘yan sanda ta cafke wata mata da zargin kisan makwabciyarta a Legas.

Matar mai suna Cynthia ta yi ajalin makwabciyarta ce mai suna Barakat kan wata ‘yar hatsaniya.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.