Trump Ya Daina Boye Boye, Ya Fadi abin da Zai Faru idan Amurka Ta Kwace Hormuz
- Shugaba Donald Trump ya ce Amurka za ta kula da mashigar ruwan Hormuz tare da neman a biya ta kuɗin tsaro da za ta ba jirage
- Trump ya zargi Iran da karya yarjejeniyar da aka cimma kan sake buɗe mashigar, lamarin da ya jawo sake musayar hare-hare
- Sai dai kuma, ita Iran ta ce ba za ta buɗe mashigar Hormuz ba har sai Amurka ta dakatar da ayyukan sojinta, yayin da rikicin ke kamari
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Sani Hamza ƙwararren edita ne a fannin nishaɗi, al'amuran yau da kullum, da kuma siyasa, wanda ke da shekaru sama da biyar a aikin jarida.
Amurka - Shugaban Amurka, Donald Trump, ya bayyana cewa ƙasarsa na shirin karɓar alhakin kula da mashigar Hormuz, yana mai cewa ya kamata ƙasashen da ke cin moriyar tsaron hanyar su biya Amurka kuɗin wannan aiki.
Trump ya bayyana hakan ne a wata hira ta wayar tarho da tashar Fox News, yayin da rikicin da ke tsakanin Amurka da Iran ke ci gaba da ƙamari.

Source: UGC
"Za mu kare mashigar kuma za a biya mu"
A cewar Trump, Amurka za ta kasance mai kula da mashigar, wadda ke daga cikin muhimman hanyoyin jigilar ɗanyen mai da iskar gas a duniya, in ji rahoton USA Today.
Ya ce:
"Za mu riƙe mashigar, kuma mai yiwuwa mu kasance masu tafiyar da ita. Za mu zama masu kula da mashigar. Wataƙila ma mu kira kanmu 'masu tsaron mashigar'. Kuma ya kamata a biya mu saboda wannan."
Trump ya ƙara da cewa ba zai dace Amurka ta ci gaba da kashe kuɗaɗe wajen kare hanyar ba tare da samun wani sakamako ba.
Ya ce ƙasashen da ke amfana da tsaron mashigar suna da ƙarfin tattalin arziki, don haka ya kamata su biya kuɗin aikin da Amurka za ta yi.
Trump ya zargi Iran da karya yarjejeniya
Aljazeera ta rahoto cewa shugaban Amurka ya kuma zargi Iran da karya yarjejeniyar da aka cimma tsakanin ƙasashen biyu kan sake buɗe mashigar Hormuz.
A cewarsa:
"Mun cimma yarjejeniya, komai ya kammala, amma daga baya suka karya ta. Kullum haka suke yi. Mun yi yarjejeniyoyi da su har sau 10, don haka za mu ɗauki mataki mai tsauri a kansu."

Source: Getty Images
Iran ta gindaya sharadi kan buɗe Hormuz
A nata ɓangaren, dakarun IRGC na Iran sun ce hanyar da za a bi wajen dawo da zirga-zirgar jiragen ruwa ta mashigar Hormuz ita ce Amurka ta dakatar da ayyukan sojinta a yankin.
Rundunar ta yi gargaɗin cewa ci gaba da abin da ta kira katsalandan daga Amurka na iya haifar da ƙarin rikice-rikice da za su shafi kasuwannin mai da iskar gas a duniya.
Iran ta ce ta kai hare-hare kan wasu sansanonin sojin Amurka da ke yankin Tekun Fasha, yayin da ta ci gaba da rufe mashigar Hormuz.
Kasar Iran ta kai hare-hare Amurka
A wani labari, mun ruwaito cewa, rundunar sojojin Iran ta IRGC ta yi ikirarin cewa ta kai wani "mummunan hari kuma na ba-zata" kan wuraren da Amurka ke amfani da su a Oman.
IRGC ta yi ikirarin kai hari kan wuraren tallafin kayan aiki da wuraren loda man fetur da jiragen ruwan yakin Amurka masu daukar jiragen sama ke amfani da su a tashar jiragen ruwa ta Duqm.
Rundunar ta yi ikirarin cewa ta lalata cibiyar bada umarni da sarrafawa tare da wurin da ake ajiye jiragen yaki marasa matuka na MQ-9 a sansanin Prince Hassan Air Base.
Asali: Legit.ng


