Jirgin Sama Dauke da Mataimakiyar Shugaban Kasa da Wasu Mutum 8 Ya Yi Hatsari

Jirgin Sama Dauke da Mataimakiyar Shugaban Kasa da Wasu Mutum 8 Ya Yi Hatsari

  • Mataimakiyar shugaban kasar Zambia, Mutale Nalumango, ta tsira ba tare da rauni ba bayan jirgin mai saukar ungulu da take ciki ya fadi
  • Mutane takwas ne ke cikin jirgin lokacin da hatsarin ya faru yayin yakin neman zaben shugaban kasa da ake gudana
  • Nalumango ta ce ba a san musabbabin hatsarin ba, yayin da gwamnatin Zambia ta tabbatar tana cikin koshin lafiya

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Zambia - Mataimakiyar shugaban kasar Zambia, Mutale Nalumango, ta tsallake rijiya da baya tare da wasu mutum bakwai bayan jirgin mai saukar ungulu da suke ciki ya yi hatsari.

Rahitanni daga Zambia sun nuna cewa cewa jirgin da ke dauke da mataimakiyar shugaban kasar ya yi hatsafi ne jim kadan bayan tashinsa yayin yakin neman zaben kasar.

Mutale Nalumango.
Wurin da jirgin mataimakiyar shugaban Zambia, Mutale Nalumango ya fado kasa Hoto: Mutale Nalumango
Source: Facebook

Jaridar Vanguard ta ruwaito vewa Zambia za ta gudanar da babban zaben shugaban kasa a ranar 13 ga watan Agustan 2026, inda ake sa ran Shugaba Hakainde Hichilema zai nemi wa'adi na biyu a mulki.

Kara karanta wannan

Wike ya tsage gaskiya kan yiwuwar PDP ta iya lashe zaben shugaban ƙasa a 2027

Yadda hatsrarin jirgin ya faru

Nalumango mai shekara 71 ta shaida wa manema labarai cewa hatsarin ya faru ne yayin da suke barin wani taron yakin neman zabe a garin Nakonde da ke Arewa maso Gabashin kasar.

Ta ce:

"Bayan jirgin ya tashi, ban san ko minti daya ko biyu ba, sai kawai muka dawo kasa. "Mutane takwas ne a cikin jirgin kuma dukkanninmu muna cikin koshin lafiya."

Mene ne ya haddasa hatsarin jirgin?

Mataimakiyar shugaban kasar ta bayyana cewa har yanzu ba a san abin da ya haddasa hatsarin ba, sai dai ta ce jirgin ya samu mummunar matsala sakamakon fadowar da ya yi.

Bayan hatsarin, Nalumango ta yi gwajin lafiya na gaggawa, inda gwamnatin Zambia ta tabbatar cewa an sallame ta daga asibiti cikin koshin lafiya.

Hotuna sun nuna yadda jirgin ya lalace

Hotunan da aka wallafa a kafafen sada zumunta sun nuna jirgin mai saukar ungulu na rundunar sojin saman Zambia a kwance gefe bayan da ake zargin ya bugi wata bishiya kafin ya fadi.

Lamarin ya haifar da fargaba yayin da yakin neman zaben shugaban kasa ke ci gaba a kasar, sai dai babu wanda ya rasa ransa ko ya samu munanan raunuka a hatsarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262