Sojojin Amurka Sun Kashe Yan Ta'adda 199 a Farmaki Gudada Suka Kawo Najeriya
- Gwamnatin Amurka ta sake fito da nasarorin da ta samu a hare-haren hadin gwiwa da ta kawo Najeriy domin kawo karshen ayyukan ta'addanci
- Wani hdimin shugaban Amurka, Sebastian Gorka dakarun kasar sun hala yan ta'addanasu ikirarin jihadi 199 a hari daya kacal
- Gorka ya ce wannan shi ne mafi girman adadin mayakan kungiyar ta'addanci da aka kashe a farmaki guda tun bayan harin 11 ga Satumba, 2001
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Mataimakin mai ba Shugaban Amurka Donald Trump shawara kuma babban daraktan yaƙi da ta’addanci a Kwamitin Tsaron Ƙasa, Sebastian Gorka, ya yi magana jan hare-haren da aka kawo Najeriya
Sebastian Gorka ya ce dakarun ƙasar Amurka sun kashe mayaka 199 na kungiyoyi ta'addanci a farmaki guda da aka gudanar a Najeriya.

Source: Twitter
Gorka ya bayyana hakan ne yayin wata hira da Marissa Streit, wadda aka fitar a ranar 24 ga Yuni, 2026, kamar yadda The Cable ta ruwaito.
Da yake magana kan yaƙin da Amurka ke yi da ta’addanci, Gorka ya ce gwamnatin Trump ta ci gaba da samun nasara kan ƙungiyoyin masu tsattsauran ra'ayin addini.
"Idan kuna barazana ga Amurkawa ko kuna kai hari kan Kiristoci saboda addininsu, shugaban kasa zai aika muku da saƙo mai ƙarfi," in ji shi.
A cewarsa, kimanin makonni uku kafin hirar, ya kalli yadda jami'an Amurka suka kashe mayakan jihadi 199 a wani farmaki da aka gudanar a Najeriya.
"Na kalli abin kai tsaye daga Situation Room. Mun kashe mayakan jihadi 199 a aiki guda a Najeriya."
Gorka ya ce wannan shi ne mafi girman adadin mayakan da aka kashe a aiki guda tun bayan harin 11 ga Satumba, 2001.
Sai dai bai fayyace ko yana magana ne kan farmakin haɗin gwiwar Amurka da Najeriya na ranar 15 ga Mayu, wanda aka ce ya kashe Abu-Bilal al-Minuki, ko kuma farmakin ranar 30 ga Mayu da aka ruwaito cewa ya kashe mayaƙan ISWAP 21 ba.
Gorka ya kuma bayyana cewa an kwaso dimbin kayayyaki daga sansanonin mayaƙan da aka kai wa hari, inda ya ce sai da aka buƙaci ƙarin jirgin sama domin ɗauko kayan saboda yawansu.
Da aka tambaye shi dalilin da ya sa aka fi mayar da hankali kan Afirka wajen yaƙi da ta’addanci, Gorka ya ce karuwar yawan Kiristoci a nahiyar na daga cikin dalilan da suka sa ƙungiyoyin jihadi ke kai hare-hare a yankin.
Ya kuma ce ƙungiyar ISIS ta yi amfani da raunin tsarin mulki da rikice-rikicen da ke yankin Sahel wajen faɗaɗa ayyukanta da yaɗa manufarta.
Asali: Legit.ng

