Hormuz: Trump Ya Zargi Iran da Gangancin Karya Yarjejeniyar Sulhu da Amurka
- Donald Trump ya zargi kasar Iran da kai wa wani jirgin ruwa hari lokacin da ya yi kokarin ya bi ta mashigar Hormuz a makon nan
- Shugaban Amurka ya zargi kasar Iran da abin da ya kira da shashanci ganin cewa an cin ma yarjejeniyar sulhu kuma an dakatar da yaki
- Wasu jirage marasa matuka ne suka kai wa jiragen ruwan harin, amma duk da haka ba a samu asarar rai ko dukiya a sanadiyyar hakan ba
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
America - Shugaban kasar Amurka Donald Trump ya zargi Iran da abin da ya kira ‘sakarcin karya yarjejeniya’ da aka cin ma bayan tsawon lokaci.
Donald Trump ya yi wannan magana ne a sakamakon hari da aka kai wa wani jirgin ruwa a lokacin da ya yi yunkurin ratsawa ta mashigar nan ta Hormuz.

Source: Getty Images
Donald Trump ya zargi Iran da harin Hormuz
Rahoton da ya fito daga tashar BBC ya bayyana cewa babu wani rai da aka rasa a sakamakon harin da aka kai wa jirgin a ranar Alhamis 25 ga Yuni 2026.
Da yake magana a shafinsa na Truth Social a yammacin Juma’a, Donald Trump ya zargi Iran da amfani da makamai wajen harbin wasu jiragen ruwa.
“Karara, an yi sakarcin karya yarjejeniyarmu.”
Donald Trump ya bayyana wa duniya cewa duk da sun rotsa jirage marasa matuki uku, wani daga cikinsu ya yi nasarar yi wa wani jirgi mai tsada rauni.
“An yi wa jirgin dameji, amma dai ya yi nasarar wucewansa.”
Gwamnatin Iran ba ta tanka Donald Trump ba
Daga lokacin da Trump ya yi wannan magana zuwa yanzu da ake tattaro rahoton nan, ba a ji Gwamnatin Iran ta maida wa Amurka martani ba.
Quartz An dai kai harin ne kwanaki kadan bayan Sojojin IRCG na juyin-juya halin kasar Iran sun yi gargaji cewa za su farmaki masu bi ta Hormuz.
Shafin Quartz ya ce bayanan da aka samu daga Birtaniya sun nuna an kai jirgin hari ne a Kudu maso gabashin kasar Oman a ranar Alhamis da ta gabata.

Source: Getty Images
Ana so a kawo karshen matsaloli a Hormuz
An ce jirgin yana ta bin shawarwarin UKMTO lokacin da aka auka masa, amma dai majiyar ta ce duka wadanda suke ciki ba su samu ko rauni ba.
Shugaban IMO ya sha alwashin hada kai da Amurka da Iran domin ganin karshen wannan lamari.
A cewar IMO, jirage da dama sun wuce ta mashigar bayan an bude Hormuz sakamakon sasantawar da Amurka ta yi da kasar Iran a watan Yulin 2026.
Sai dai an ji mahukuntan kasar Iran sun dage cewa duk wanda zai bi ta mashigar sai ya biya kudi, zancen da Donald Trump bai yi na’am da shi ba.
Lokacin da Iran ta Hormuz
Ana da labari kasar Iran ta bayyana cewa ta hana jiragen yaki na Amurka da Isra'ila shiga mashigar Hormuz amma kasar ta musanta wannan ikirarin.
Hakan ta faru ne bayan Donald Trump ya sanar da cewa Amurka za ta jagoranci fitar da jirage da suka makale a mashigar, abin da Iran ta ce karya yarjejeniya ne.
Rundunar Amurka ta tabbatar cewa ba wani jirgin nata da aka kai wa hari, tana ci gaba da ayyukanta na toshe hanyoyin jiragen ruwan Iran yayin da ake ta yaki.
Asali: Legit.ng

