Siyasar Najeriya
A ranar Juma’a ne Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta fitar da jerin sunayen wadanda aka tantance a matsayin 'yan takarar zaben gwamnan Anambra.
Gwamna Aminu Tambuwal na jihar Sakkwato ya caccaki majalisar dattijai kan yadda ta damka ikon da kundin tsarin mulki ya bai wa INEC ga Hukumar Sadarwa ta NCC.
Hadiin gwamnan jihar Legas kan magudanan ruwa da albarkatun ruwa, Joe Igbokwe, ya ce abubuwa za su daidaita idan Bola Tinubu, ya zama shugaban kasar Najeriya.
Saboda shirya taron siyasa a yayin hare-haren ‘yan fashi a Zamfara, majalisar dokokin jihar ta gayyaci mataimakin gwamnan, Mahdi Gusau da kwamishinan yan sanda.
Ɗan majalisar wakilan tarayya, Kabiru Amadu, daga jihar Zamfara ya bayyana ficewarsa daga PDP zuwa jam'iyya mai mulki APC, domin bin sawun gwamna Matawalle.
Yayin da ake shirin gudanar da zaɓen ƙananan hukumomi a jihar Ogun, gwamnan jihar ya buɗe fagen yaƙin neman zaɓe na jam'iyyar APC a ƙaramar hukumar Imeko Afon.
Muhammad Buhari a ranar Alhamis, 10 ga Yuni, yayin wata hira ya ce, babu wanda ke da ikon yanke hukunci ga jam’iyya mai mulki ta APC kan mulkin karba-karba.
Bayan ficewarsa daga jam'iyyar APC a shekarar 2020 biyo bayan rashin ba shi tikitin takara, Gwamnan jihar Edo, Godwin Obaseki, yace ba zai taba komawa APC ba.
Sanannen ɗan siyasar nan kuma tsohon sanatan Kaduna ta tsakiya, Shehu Sani, ya bayyana ficewarsa daga jam'iyyar PRP, sai dai bai ce komai ba game da inda yakoma
Siyasar Najeriya
Samu kari