Jihar Niger
Jagora a APC, Dr. Mohammed Santuraki ya zargi gwamnatin tarayya da nuna bangaranci ga Neja a nadin shugabannin Hukumar Raya Arewa ta Tsakiya (NCDC).
Dan majalisar wakilai daga jihar Neja, Hon Adamu Lokoja, ya sauya sheka daga jam'iyyar PDP zuwa APC. Ya samu tarba daba shugabannin APC na jihar.
Jam'iyyar APC a jihar Neja ta kara ƙarfi da manyan kusoshin adawa ciki har da mutum 2 da suka nemi zama gwamna a 2023 suka baro jam'iyyunsu zuwa cikinta.
Mutane da dama sun rarrabu kan furucin Gwamnan Niger, Mohammed Umar Bago da ya janyo cece-kuce bayan shiga cikin cocin Living Faith a Minna da ke jihar.
Gwamnan Neja, Mohammed Umaru Bago ya bayyana akwai bukatar cure mutane daga ƙangin talauci da yaƙi da jahilci domin kawo ƙarshen matsalar tsaro a ƙasar nan.
Gwamnan jihar Neja, Muhammed Umaru Bago ya karyata jita-jitar da ke yawo cewa ba ya ga maciji da mataimakinsa, Yakubu Garba, ya ce kansu a haɗe yake.
UB Shehu ya rasa matarsa bayan an dauke wuta yayin da ake tsaka da yiwa matarsa tiyata a Neja, sannan janareto bai yi ki ba, lamarin ya dauki awa 11.
Rikicin siyasa ya ɓarke tsakanin gwamnan jihar Neja, Bago da mataimakinsa Yakubu Garba, wanda aka ce ya fara kwashe kaya daga gidan gwamnati, da zummar barin aiki.
Mataimakin gwamnan jihar Neja, Kwamared Yakubu Garba, ya fito ya yi magana kan rahotannin da ke cewa ya yi murabus daga mukaminsa. Ya ce ba gaskiya ba ne.
Jihar Niger
Samu kari