Masu Garkuwa Da Mutane
Rundunar 'yan sandan jihar Neja ta bayyana cewa an samu nasarar cafke daya daga cikin mutanen da su ka kai hari tare da garkuwa da mutane a jihar.
Gwamna Uba Sani na jihar Kaduna ya bayyana cewa dole ce ya sa ya yi sulhu da 'yan ta'adda da su ka addabi mazauna kananan hukumomi daban-daban na jihar.
Gwamnatin jihar Anambra ta rusa wani hotel da aka mayar da shi maboyar masu garkuwa da mutane. Ana zargin suna birne mutane, an samu kaburbura 30.
Rundunar tsaron Najeriya ta sanar da kashe mataimakin Bello Turji mai suna Aminu Kanawa yayin farmaki. An kashe wasu tarin mayakan dan ta'addar a Sokoto da Zamfara.
Rahotanni sun bayyana cewa an sace fastoci uku a jihar Kogi bayan sun yi wa’azi. Masu garkuwar na neman Naira miliyan 20 a matsayin kudin fansar malaman.
Gwamnan Anambra, Soludo, ya kaddamar da rundunar tsaro ta "Udo Ga-Achi" tare da bayar da kyautar Naira miliyan 5 ga masu bayar da bayanai kan 'yan ta'adda.
Wasu mahara da ake zargin masu garkuwa ne sun sace matar mataimakin sufetan ƴan sanda na ƙasa mai ritaya a gidanta da ke jihar Ogun a ranar Juma'a.
'Yan sanda sun kama Muttaka Garba da Yusuf Usman kan yin garkuwa da kashe wani yaro, Salihu Sadi a Dankama, inda suka nemi fansa Naira miliyan 25 kafin kashe shi.
Ƴan bindiga sun kai hari asibitin Kankara da ke jihar Katsina inda suka harbi wani likita tare da yin garkuwa da wasu mutane 5. Jami'an tsaro sun bi bayan miyagun.
Masu Garkuwa Da Mutane
Samu kari