Manyan Labarai A Yau
A ƙarshen shekarar 2025, Farfesa Mahmud Yakubu zai sauka daga kujerar shugabancin hukumar INEC bayan shafe wa'adi biyu kamar yadda doka ta tanada.
Gwamnonin jam'iyyar APC mulki a Najeriya sun ziyarci tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari a Kaduna. Sun bukaci ya tsoma baki kan ficewar na kusa da shi.
Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya koka kan ksruwar hare-haren 'yan ta'addan Boko Haram a jihar. Ya ce lokaci ya yi da za a fadi gaskiya.
Sanata Sunday Karimi mai wakiltar Kogi ta Yamma ya taso Sanata Ali Ndume a gaba kan kalaman da ya yi dangane da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.
Farfesa Mahmud Yakubu ya jagoranci taron INEC yayin da ake yada jita-jitar tsige shi. INEC ta ce saƙon WhatsApp da ke yawo ba gaskiya ba ne kwata-kwata.
Obi na Onitsa, mai martaba Nnaemeka Achebe, ya yi magana kan rahotannin da ke cewa ya yi wa 'yan Arewa kashedi kan kisan da aka yi wa mafarauta a Edo.
Shugaban kamfanin MTN na farko kuma attajirin ɗan kasuwa da ya kafa bankin Diamond, Pascal Gabriel Dozie ya kwanta dama, mun haɗa maku abubuwan sani gane da shi.
Gwamnan jihar Kaduna, Uba Sani, ya tuna da ma'aikatan da suka yi ritaya da wadanda suka rasu. Gwamnan ya umarci a fitar da kudade domin biyansu hakkokinsu.
Naira ta fadi zuwa N1,629/$ a kasuwar NFEM duk da tallafin CBN. Bukatar dala daga 'yan kasuwa da masu zuba jari na ci gaba da haifar da matsin lamba ga Naira.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari