Zaben jihohi
Yayin da aka fara sauraran shari’ar zaben gwamnan jihar Kogi, kotu ta soke karar jam’iyyar APP da ke kalubalantar zaben Gwamna Ododo na jam'iyyar APC.
An rasa gane wanene halataccen 'dan takaran APC a zaben Gwamnan Edo domin kuwa an ba Hon. Dennis Idahosa, Sanata Monday Okpebholo da Anamero Sunday Dekeri tikiti.
Dennis Idahosa, dan Majalisar Tarayya ya samu nasarar kasancewa dan takarar gwamna a jihar Edo bayan gudanar da zaben fidda gwani a yau Asabar a jihar.
Yayin da ake shirin gudanar da zabe, jam’iyyar APC na neman kwace kujerar gwamnan Anambra karfi da yaji wurin matsa wa gwamnan ya koma jam'iyyar APC.
Kasa da awanni 24 kafin gudanar da zaben fidda gwani a gobe Asabar, dan takarar gwamna a APC, Fasto Osagie Ize-Iyamu ya janye daga takarar gwamnan jihar Edo.
Hukumar zabe ta ƙasa INEC ta ce wasu 'yan daba sun hargiza zaben cike gurbi da jami'an hukumar ke gudanarwa a jihar Enugu, an lalata kayayyakin zabe gaba daya.
Rahotannin da ke shigo mana yanzu na nuni da cewa misalin karfe 1:58 na ranar Laraba aka rantsar da Duoye Diri a karo na biyu a matsayin gwamnan jihar Bayelsa.
Oluwole Oke, dan majalisar wakilai, ya gabatar da kudirin kafa sabbin jihohi uku a shiyyar kudu maso yammacin kasar, sun hada da; Oke-Ogun, Ijebu, da Ife-Ijesa.
Tsohon mamban Majalisar jihar Ondo, Hon. Tomide Akinribido ya watsar da kashin jam’iyyar PDP tare da komawa APC mai mulkin jihar a jiya Juma'a 9 ga watan Faburairu.
Zaben jihohi
Samu kari