Zaben jihohi
Ranar Jumu'a, 12 ga watan Janairu, kotun koli ta zaɓi yanke hukunci kan nasarar gwamnonin jihohin Kano, Legas, Bauchi, Zamfara, Filato, Kuros Riba da Ebonyi.
Yayin da ke daf da yanke hukuncin karshe a shari'ar zaben gwamnan jihar Plateau, jami'yyar PDP ta shiga taitayinta inda ta ce a tashi da azumi don neman nasara.
Yayin da ake shirye-shiryen gudanar da zabe a jihar Edo, Dan Majalisar Tarayya, Hon. Anamero Dekeri ya nuna sha'awar tsayawa takara a jam'iyyar APC.
Rundunar 'yan sanda a jihar Kano ta gargadi jama'ar jihar kan tada tarzoma inda ta ce za ta murkushe duk wani yunkurin tada hankulan jama'a a jihar.
Kotu mai daraja ta ɗaya a Najeriya ta kammala sauraro karar zaben gwamnan jihar Kuros Riba kuma bayanai sun nuna zata sanar da hukuncinta gobe Jumu'a.
Mai shari'ar Okoro, shugaban kwamitin mutum biyar na Kotun Koli ya yanke hukunci kan shari'ar zaben gwamnan jihar Adawa. Ya tabbatar da nasarar Ahmadu Fintiri.
Mun ji labari an shigar da kara a kan ‘yan kungiyar Omoluabi a Osun. APC ta zargi tsohon gwamna Rauf Aregbesola da zagon-kasa har an maka kungiyarsu a kotu.
Kotun kolin Najeriya ta shirya raba gardama kan zaben gwamnan jihar Kano, Legas da wasu jihohin ranar Jumu'a, za kuma ta zauna kan wasu kararraki a makon nan.
An sake samun hatsaniya bayan an zabi dan tsohon Sifetan 'yan sanda a matsayin wanda zai gaji kujerar Ministan Tinubu bayan ya yi murabus daga kujerar.
Zaben jihohi
Samu kari