Labaran garkuwa da mutane
Rahotanni sun bayyana cewa 'yan bindiga sun shiga wani kauyen karamar hukumar Sabon Gari da ke jihar Kaduna, sun sace uwa da ɗanta, amma mijin ya tsere.
Rundunar yan sandan jihar Kwara ta bayyana cewa jami'an tsaron haɗin guiwa sun yi nasarar kama mutum 3 da ake zargi da hannu a sace basarake da wasu uku.
'Yan bindiga sun kashe wani magidanci mai suna Tijani Amedu tare da yin garkuwa da kananan yara 13 a hanyar Kaduna, kuma sun nemi kudin fansa naira miliyan 60.
Doka ta haramta tara kudi a biya ‘yan bindiga a Najeriya. Muhammad Badaru Abubakar ya ce idan ana biyan fansa, ‘yan bindiga ba za su daina ta’adi a Najeriya ba.
Ministan Tsaron Najeriya, Badaru Abubakar ya gargadi 'yan Najeriya kan biyan kudaden fansa ga 'yan bindiga inda ya ce hakan kara lamarin zai yi a kasar.
Rahotanni daga iyalan shugaban ƙaramar hukumar Ukum ta jihar Benuwai wanda ke hannun masu garkuwa, sun nuna cewa maharan sun nemi kuɗin fansa N50m.
Yan bindigar da suka yi garkuwa da mutum 23 a kauyen Kawu da ke yankin Bwari a babban birnin tarayya Abuja sun tuntubi yan uwansu. Sun nemi kayan abinci da babura 5.
Sanata Shehu Sani ya ba da labarin wani tsohon shugaban makaranta da yan bindiga suka kama yayin da ya ke kai kudin fansar wani. Shi ma an nemi a kai kudin fansa.
Shugaban ASUU reshen jihar Kebbi ya tabbatar da yin garkuwa da babban malamin jami'ar kimiyya da fasaha da ke Alieru, har yanzun ƴan sanda ba su yi magana ba.
Labaran garkuwa da mutane
Samu kari