Labaran garkuwa da mutane
Rahotanni sun bayyana cewa 'yan bindiga sun kashe wata Nabeeha Al-Kadriyar, daya daga cikin mata shida 'yan gida daya da suka yi garkuwa da su a birnin tarayya Abuja
‘Yan bindiga sun sake yin garkuwa da wani malamin jami'ar tarayya da ke Gusau, jihar Zamfara, bayan da suka kutsa gidansa a safiyar ranar Laraba.
Kimanin mutane 85 ne ‘yan bindiga suka sace a jihar Kaduna a hare-haren da aka kwashe kwanaki hudu ana kai musu. 'Yan sanda sun mayar da martani.
Bayan sama da watanni 10, yan bindiga sun dawo da ayyukansu a kan babban titin Kaduna zuwa Abuja, sun yi garkuwa da mutane 30 a ranar Lahadi, 7 ga watan Janairu.
Rahotanni sun bayyana cewa 'yan bindiga sanye da kayan Fulani sun kai hari Sagwari da ke Abuja, sun sace mutum 10. Sun kai harin karfe 7:30 na yammacin ranar Lahadi,
Wasu miyagun yan bindiga sun halaka magajin garin Wuro Musa da suka sace a jihar Taraba ranar Jumu'a. An kashe manomi tare da sace wasu kauyukan Kaduna.
Masu garkuwa da mutanen da suka sace Alhaji Mansoor Al-Kadriyar da yaransa shida sun tuntubi yan uwansu, inda suka bukaci a biya kudin fansa naira miliyan 60.
Tsagerun yan bindiga sun yi awon gaba da mai martaba Eze Samuel Agunwa Ohiri, a gaban gidansa da ke Orodo, karamar hukumar Mbaitoli ta jihar Imo.
Sanata Karimi na Kogi ta Yamma ya bayyana cewa sha'anin tsaro na neman faskara a mazaɓarsa cikin yan kwanakin nan musamman batun garkuwa da mutane.
Labaran garkuwa da mutane
Samu kari