Magana Ta Ƙare, Shugaba Tinubu Ya Ɗauki Wanda Zai Masa Takarar Mataimaki a Zaben 2027
- Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya kawo karshen duk wata jita-jita da jama'a ke yaɗa wa kan wanda zai dauka a matsayin abokin takara a zaben 2027
- Rahotanni sun nuna cewa kwamitin gudanarwa na APC ta ƙasa ya shiga ganawa domin tabbatar da Kashim Shettima a matsayin abokin takarar Tinubu
- Wasu shugabannin APC sun tabbatar da cewa Tinubu ya sake daukar mataimakinsa a karo na biyu, za su nemi tazarce kan mulki a babban zabe mai zuwa
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Abuja, Nigeria - Rahotanni sun nuna cewa shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ya dauki Sanata Kashim Shettima a matsayin wanda zai yi masa takarar mataimakin shugaban kasa a jam'iyyar APC.
Wannan mataki na nufin Shugaba Tinubu da mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima za su nemi tazarcen kujerunsu a zaben 2027.

Source: Facebook
DW Hausa ta tabbatar da hakan a wani rahoto da ta wallafa a shafinta na Facebook yau Juma'a, 10 ga watan Yuli, 2026.
Shugabannin APC sun shiga taro a Abuja
An ruwaito cewa kwamitin gudanarwa (NWC) na jam'iyyar APC ta kasa tare da manyan shugabannin jam'iyyar na gudanar da taro a otal din Continental da ke Abuja domin gabatar tabbatar da ɗaukar Shettima.
Bayanai sun nuna cewa taron zai ayyana Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima, a matsayin abokin takarar Shugaba Bola Ahmed Tinubu a zaben 2027.
Matakin ya zo ne bayan watanni ana rade-radin cewa Shugaba Tinubu na iya sauya Shettima da wani Kirista daga Arewacin Najeriya a matsayin mataimakinsa gabanin babban zabe mai zuwa.
Jam'iyyar APC ta tabbatar da Shettima
Wasu manyan shugabannin APC da ke wajen taron sun tabbatar wa wakilin jaridar Punch cewa Shugaba Tinubu ya sake zabar Kashim Shettima a matsayin abokin takararsa.
Sun bayyana cewa jam'iyyar za ta sanar da wannan matsaya a hukumance a yau Jumu'a, 1 ga watan Yuli, 226 domin kawo karshen duk wata jita-jita da ta shafi batun ɗan takarar mataimakin shugaban kasa na APC.
Ana sa ran sanarwar za ta kara fayyace matsayin jam'iyyar APC mai mulkin kasa yayin da shirye-shiryen tunkarar babban zaben shekarar 2027 ke ci gaba da daukar zafi a Najeriya.
Karin bayani na nan tafe...
Asali: Legit.ng

