Labaran garkuwa da mutane
An gargadi Shugaban kasa Bola Tinubu kan tashin hankalin da zai dabaibaye gwamnatinsa a sabon hasashen da Primate Elijah Ayodele ya saki bayan sace shugaban PDP.
Yan bindiga sun sace mataimakin VC na jami'ar jihar Abiya watau ABSU yayin da ya tsaya shan mai a wani gidan mai tare da mai ɗakinsa, babu wani bayani har yanzu.
Rahotanni sun nuna cewa wasu da ba a san ko su waye ba sun yi awon gaba da shugaban jam'iyyar PDP na jihar Legas a titin zuwa Ibadan jiya Alhamis da yammaci.
Wasu gwamnoni akalla 9 a Najeriya sun tabbatar da aniyarsu ta zartar da hukuncin kisa ko ɗaurin rai da rai kan duk wanda aka kama da laifin garkuwa da mutane.
Jami'ar Bayero da ke Kano ta musanta rahoton da ake yaɗawa cewa an yi garkuwa da mutane a harabar jami'ar da ke cikin birnin Kano, ta ce labarin kanzon kurege ne.
Yan sanda sun kama mata da miji da suka yi karyar an yi garkuwa da su don su samu kudin fansa har naira miliyan biyar da nufin sayen gida a Badagry da ke Legas.
Dakarun rundunar sojin Najeriya da haɗin guiwar yan banga sun ceto mutum 4 yayin da suka kai samame mafakarsu a kauyen Sabon Birni, jihar Kebbi jiya.
Shehu Sani ya tabbatar da sakin tsohon shugaban wata makaranta a Kaduna a ranar Talata, 23 ga watan Janairu. An tsare shi a lokacin da ya je kai kudin fansa.
Wasu tssgerun ƴan bindiga sun yi ajalin magajin garin wani ƙauye a yankin ƙaramar hukumar Munya ta jihar Neja, sun yi garkuwa da wasu mazauna garin su 16.
Labaran garkuwa da mutane
Samu kari