Masu Garkuwa da Mutane Matsorata Ne, Sun Cancanci Hukuncin Kisa, Remi Tinubu Ta Magantu a Bidiyo

Masu Garkuwa da Mutane Matsorata Ne, Sun Cancanci Hukuncin Kisa, Remi Tinubu Ta Magantu a Bidiyo

  • Matar Shugaban kasar Najeriya, Sanata Oluremi Tinubu, ta bukaci a yankewa masu garkuwa da mutane hukuncin kisa
  • Ta bayyana hakan ne yayin da take martani kan sace dalibai da malamai 200 a jihar Kaduna da mata 200 a jihar Borno
  • Matar Shugaban kasa ta bukaci gwamnoni da ‘yan majalisa da su kawo dokar da za ta tabbatar da hukuncin kisa kan miyagun

Aisha Musa ta shafe tsawon shekaru tana kawo labaran Hausa a bangaren siyasa, tsegumi da al’amura

Matar Shugaban kasa Oluremi Tinubu ta bayyana masu garkuwa da mutane a matsayin matsorata.

Ta jaddada cewar ya kamata duk wanda aka kama da wannan laifi ya fuskanci hukuncin kisa.

Matar Tinubu ta nemi a dunga kashe masu garkuwa da mutane
Remi Tinubu ta nemi kashe masu garkuwa da mutane Hoto: Oluremi Tinubu
Asali: Twitter

Wannan martanin na zuwa ne kan lamuran da suka faru a baya-bayan nan, da suka hada da sace mata 200 a jihar Borno da kimanin dalibai da malamai fiye da 280 a jihar Kaduna.

Kara karanta wannan

Kiran juyin mulki: Minista ya dauki zafi, ya bada umarni ga jami'an tsaro a dauki mataki

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

“Duk wanda yake garkuwa da matasa bai da lafiya, mugu ne kuma matsoraci.
“Abin ya isa haka kuma ina kira ga gwamnonin jiha cewa da zarar mun kama su a hannu, sun cancanci hukunci mai tsauri.
“Me zai ka su je ku dauke su daga makarantu? Yanzu, ina ganin abin ya isa haka. A matsayina na tsohuwar ‘yar majalisar tarayya, na yarda cewa duk wanda aka kama cikinsu ya cancanci hukunci mai tsauri.”

- Remi Tinubu

Ga bidiyon a kasa:

Yadda 'yan bindiga suka farmaki makarantar Kaduna

A baya Legit Hausa ta rahoto cewa an samu tashin hankali a garin Kuriga da ke karamar hukumar Chikun ta jihar Kaduna.

Hakan ya faru ne sakamakon harin da wasu 'yan bindiga suka kai makarantar firamare ta LEA, Kuriga (1) tare da sace dalibai da dama.

Kara karanta wannan

Ban taba ganin irinsa ba, Hadimin Tinubu ya fadi lokacin da Tinubu ke kwanciya duk daren Allah

An gano yawan yaran da aka sace a Kaduna

A halin da ake ciki, mun ji cewa shugaban makarantar firamare ta LEA da ke Kuriga a karamar hukumar Chikun a jihar Kaduna, Sani Abdullahi ya tabbatar da cewa dalibai 287 na makarantar ne wasu ‘yan bindiga sun yi garkuwa da su.

Mallam Abdullahi na daga cikin wadanda 'yan bindigar suka yi awon gaba da shi amma daga baya ya tsere tare da wasu dalibai.

Shugaban makaranta ya ba da labarin yadda 'yan bindiga suka sace dalibai 287 a Kaduna.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng