Zaben Najeriya
Dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar Labour Party a zaben 2023, Peter Obi ya yi alkawarin bunkasa harkar noma a arewa domin fitar da mutanen yankin a talauci.
Mista Peter Obi, dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar Labour Party, ya lissafa matsalolin da ya ke ganin sune ke adabar Najeriya kuma suka hana ta cigaba.
Kwamishinan Zabe na jihar Kano, Ambasada Zango Abdu, ya tabbatar da cewa za a yi zaben gaskiya da adalci a Kano inda yace mutum 5,927,656 ne suka yi rijista.
IGP na rundunar yan sandan Najeriya, Usman Alkali Baba ya bayyana cewa wasu gwamnoni na daukan nauyin yan daba domin kaiwa abokan hamyarsu hari yayin kamfen.
Sanata Godswill Akpabio ya sha alwashin daukaka kara har zuwa kotun koli kan hukuncin kotu daukaka kara da ta umarci INEC ta cire sunansa matsayin ‘dan takara.
Kwankwaso, ‘dan takarar shugabancin kasa a jam’iyyar APC, ya sanar da cewa Najeriya tana da kudin kula da ‘yan kasarta, bai dace ana aro don biyan albashi ba.
Primate Ayodele, jagoran cocin INRI Evangelical Spiritua, ya shawarci shugaban kasar Najeriya Muhammadu Buhari da yayi kokari ya sasanta da yan awaren kasar.
Primate Ayodele ya aika sakon gargadi ga shugaban hukumar INEC inda ya bukace shi da kada ya yarda jam’iyyun siyasa su hana amfani da na’urar BVAS a zaben 2023.
Reshen mata na kungiyar dalibai musulmin Najeriya, MSSN, na jihar Legas tace yan takarar da zasu kare musu hakinsu da suka hada da damar saka hijabi zasu zaba.
Zaben Najeriya
Samu kari