Yan ta'adda
A ranar Litinin, Sanata Ifeanyi Ubah ya tabbatar da mutuwar wasu daga cikin hadimansa da masu tsaron lafiyarsa a yayin wani farmaki da aka kai wa tawagarsa.
Wata kungiyar hadinn guiwa ta farar hula dake tabbatar da tsaro a karamar hukumar Batsari ta jihar Katsina ta dakile farmakin 'yan ta'adda a garin Batsari.
Alamun da suka bayyana a cikin kwanakin karshen makon nan shi ne, ta yuwu a gurfanar da mai sasanci da 'yan bindiga, Tukur Mamu, kotu a Abuja ranar Litinin.
Hukumar sojojin Najeriya ta bayyana cewa har yanzu akwai sauran yan matan makarantar Chibok da ke jihar Borno guda 98 tsare a hannun yan ta’addan Boko Haram.
Jami'an rundunar yan sandan Najeriya reshen jihar Zamfara sun yi nasarar kama wani mai suna Isiyaku Babangida, kasurgumin dan bindiga da ake nema ruwa a jallo.
Hedkwatar tsaro a ranar Alhamis ta bayyana cewa dakarun Operation Hadin Kai sun cafke mai kai wa 'yan ta'adda bayanan sirri a yankin Asokoro dake FCT, Abuja.
Alhaji Tukur Mamu mazaunin Kaduna ne kuma mawallafin jaridar Desert Herald wanda ya assasa sasanci tsakanin ‘yan bindiga da iyalan wadanda aka yi garkuwa da su.
Majiyoyi sun ce baya ga alaka da 'yan ta'addan Najeriya, Mamu ya shiga hannun hukuma ne saboda alakarsa da wata kungiyar ta'addanci a yankin Sinai dake Misra.
Ummi na tsaye a gefen wani banki lokacin da yan bindiga suka kai farmaki bankuna uku a jihar Kogi a ranar Talata, 6 ga watan Satumba, harbi bingiga ya same ta.
Yan ta'adda
Samu kari