A Yi Hattara: Katsina, Sokoto da Wasu Jihohi 25 Za Su Fuskanci Ambaliyar Ruwa
- Hukumar NiMet ta yi gargadin cewa jihohi 27 na iya fuskantar ambaliyar gaggawa tsakanin 1 zuwa 10 ga Yulin 2026 sakamakon mamakon ruwan sama
- Hukumar ta ce kasa ta riga ta koshi da ruwa bayan mamakon daminar Yuni, lamarin da zai iya haddasa ambaliya a birane da yankunan kwari
- NiMet ta bukaci jama'a su guji shiga ruwan ambaliya, su tsaftace magudanan ruwa, yayin da hukumomin agaji suka kara shirin tunkarar lamarin
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Sani Hamza ƙwararren edita ne a fannin nishaɗi, al'amuran yau da kullum, da kuma siyasa, wanda ke da shekaru sama da biyar a aikin jarida.
Abuja - Hukumar Kula da Yanayi ta Najeriya (NiMet) ta yi gargadin cewa jihohi 27 na kasar nan na iya fuskantar ambaliyar gaggawa tsakanin ranar 1 zuwa 10 ga watan Yulin 2026.
Hukumar ta bayyana cewa ana sa ran mamakon ruwan sama zai ci gaba da sauka a wannan lokaci, yayin da damina ke shiga kololuwarta a fadin kasar.

Source: Getty Images
Jihohi 27 za su fuskanci ambaliya
A cikin sanarwar da ta fitar, NiMet ta ce yawan ruwan saman da aka samu a watan Yuni ya sa kasa ta riga ta koshi da ruwa, wanda hakan ya rage karfinta na tsotse karin ruwan sama, in ji rahoton Punch.
Hukumar ta ce hakan na kara yiwuwar aukuwar ambaliyar gaggawa, musamman a yankunan kwari, birane, wuraren bakin teku da kuma wuraren da ba su da ingantattun magudanan ruwa.
Jihohin da abin zai fi shafa
NiMet ta ce jihohin da ke cikin hadarin sun hada da Taraba, Sokoto, Borno, Zamfara, Kebbi, Katsina, Kaduna, Nasarawa, Plateau, Adamawa, Kwara, Kogi, Oyo, Ogun, Legas, Osun, Ekiti, Delta, Edo, Abia, Imo, Anambra, Enugu, Akwa Ibom, Cross River, Rivers da Bayelsa.
Illolin da ake sa ran za su biyo baya
Hukumar ta yi gargadin cewa mamakon ruwan saman na iya haddasa cunkoson ababen hawa, rufe hanyoyi da kawo tsaiko ga harkokin sufuri.

Kara karanta wannan
Peter Obi ya nuna damuwa kan gargadin da Majalisar ɗinkin duniya ta yi wa Arewacin Najeriya
Ta kuma ce ana iya samun katsewar wutar lantarki da hanyoyin sadarwa a wasu wurare, yayin da rashin gani sosai a lokacin ruwan sama zai iya jefa direbobi da jiragen sama cikin hadari.
Bugu da kari, NiMet ta ce ambaliyar na iya lalata gonaki, haddasa asarar amfanin gona tare da lalata hanyoyi, gadoji, magudanan ruwa da sauran kayayyakin more rayuwa.
NiMet ta ba da shawarwari
Hukumar ta bukaci 'yan Najeriya su rika bibiyar hasashen yanayi da gargadin ambaliya, tare da tabbatar da tsaftace magudanan ruwa domin saukaka kwararar ruwa.
Haka kuma ta shawarci jama'a da su guji tafiya ko tuki cikin ruwan ambaliya, su tabbatar sun tsare kayayyakin da ke waje, sannan su karfafa gine-ginen da ka iya fuskantar hadari.
NiMet ta kuma bukaci hukumomin bayar da agajin gaggawa kamar NEMA, SEMA da shugabannin al'umma su kara shirye-shiryen tunkarar yiwuwar ambaliyar domin rage asarar rayuka da dukiyoyi.
Asali: Legit.ng
