Ku Samo Mana Babura 2 da Kayan Abinci, ’Yan Bindiga Ga Mazauna Kaye a Jihar Kaduna
- 'Yan bindiga sun nemi a basu kayan abinci a madadin kudin fansa da suka nema daga dangin wadanda suka sace
- Sun ce a basu babura da kayan abinci da barasa kafin su sako mutanen tunda sabbin kudi sun gagara samuwa
- Ana kyautata zaton sauya kudin Najeriya zai kawo karshen matsalar rashin tsaro da ake ciki a kasar nan
Jihar Kaduna - Wadanda suka yi garkuwa da wasu mutum 14 a kauyen Janjala a karamar hukumar Kagarko ta jihar Kaduna sun nemi a basu babura sabbi guda biyu, kayan abinci, kwaya da barasa kafin su sako mutanen da suka sace.
City & Crime ta ruwaito cewa, ‘yan bindiga a makon jiya sun sako mutum daga 11 da suka sace a kauyen makwabta da ke kusa da Kadara bayan karbar kayan abinci, kwaya da barasa a matsayin fansa.

Kara karanta wannan
Bidiyon Yadda Aka Yi Bushasha Da Bandir-Bandir Din Sabbin Kudi a Wajen Wani Buki Yayin da Ake Nemansu Ido Rufe

Asali: UGC
Wannan karbar kayan abinci na zuwa ne bayan da suka ki karbar tsoffin kudade N5.3m da aka basu domin sakin mutanen, rahoton Daily Trust.
A bamu babura da abinci - bukatar 'yan bindiga
‘Yan bindigan sun ki sakin sauran mutum tara tare da cewa, dole sai an tara musu kudin fansan da ya kai N30m na sabbin kudi.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Da yake magana ta wayar salula, sakataren sarkin Janjala, Babangida Usman ya ce, shugaban ‘yan bindigan ya ce, tunda an gaza sama musu sabbin kudi, to a siya musu sabbin babura da kayan abinci.
A cewarsa:
“Don haka, wannan shine yanayin da ahalin wadanda aka sace suke ciki. Kuma ta yaya za a samu kudin siyan babur da kayan abincin ma wata matsalar ce.”
Ya zuwa yanzu dai ba a samu jin ta bakin kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Kaduna ba, Muhammad Jalige.

Kara karanta wannan
Ba Zamu Karba Kudin da Zasu Zama Takardun Tsire ba: 'Yan Bindiga Sun ki Karbar Tsofaffin N5.3m na Fansa a Kaduna
'Yan kasuwa a Kebbi sun koka kan karancin sabbin Naira
A wani labarin, kunji yadda 'yan kasuwa a jihar Kebbi suka bayyana kokensu kan yadda sabbin kudade ke ka kin samuwa a jihar.
A cewarsu, za su rufe kasuwancinsu saboda babu yadda za su yi su samu abin da suke bukata daga kwastomominsu.
Wannan na zuwa ne daidai lokacin da aka gaza samun sabbin kudi a bankuna gashi kuma ana kokarin daina amfani da tsoffin kudaden da ake dasu a hannu.
Asali: Legit.ng