Yan ta'adda
Shugaba Bola Tinubu ya yi kus-kus da Gwamna Dauda Lawal Dare na jihar Zamfara inda ya bukaci bayanai kan tsaro domin tabbatar da kawo karshen matsalar.
Gwamna Mohammed Umar Bago ya kafa dokar ta baci a jihar kan ayyukan 'yan daba yayin da jihohin Arewa ke fama da ‘yan daba da suke kawo matsala a jihohi.
Gwamnatin jihar Borno ta tuna da ragowar 'yan matan Chibok da ke tsare a hannun Boko Haram. Gwamnatin ta sha alwashin ceto su domin sada su da iyalansu.
An bayyana yadda wasu mahara suka hallaka mutane suna tsaka da bacci a jihar Plateau, lamarin da ya jawo firgici da tashin hankali a jihar. An bayyana yadda ta faru.
Dakarun sojojin Najeriya sun samu nasarar cafke wasu bata garin mutane wadanda ke yi wa 'yan ta'addan Boko Haram safarar kayayyaki a jihar Borno.
Karamin ministan tsaro Bello Muhammad Matawalle, ya yaba sojojin Najeriya kan nasarorin da suke samu na sheke 'yan ta'adda. Ya ce za su kawo karshen matsalar.
An fafata a tsakanin mayakan kungiyoyin ta'addanci na ISWAP da Boko Haram. Kazamin fadan da 'yan ta'addan suka fafata ya jawo an kashe tsageru masu yawa.
Yayin da ake fama da matsalar ta'addanci a Najeriya, Kungiyar Dattawan Kiristoci ta ce wasu mutane ne daga kasashen ketare ke kawo matsalar tsaro a Najeriya.
Rundunar sojojin Najeriya ta na ci gaba da samun nasara kan 'yan ta'adda bayan sake cafke kasurgumin dan ta'adda da ke nema ruwa a jallo a jihar Adamawa.
Yan ta'adda
Samu kari