2027: An Yi Hasashen Jihohin da Atiku Zai Lashe a Zaɓe, Arewa Za Su ba Shi Ƙuri'u
- Kungiyar Political Intelligence Group ta yi hasashen yawan jihohin da Atiku Abubakar zai lashe a zaɓen 2027
- Hasashen ya nuna Atiku zai samu nasara a jihohi da dama daga Arewacin Najeriya yayin Peter Obi zai lashe jihohi takwas
- Kungiyar ta ce hasashen ya dogara ne kan halin siyasar yanzu, kuma sauye-sauyen tattalin arziki, hadaka na iya sauya sakamakon kafin 2027
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.
Abuja - Kungiyar Political Intelligence Group (PIG) ta fitar da wani hasashe da ke nuna cewa Atiku Abubakar zai iya lashe jihohi tara a zaben shugaban kasa na 2027.
An bayyana wannan hasashe ne yayin da ake shirye-shiryen gudanar da zaben shekarar 2027 a Najeriya.

Source: Twitter
Legit.ng ta ruwaito cewa hasashen, wanda aka wallafa a Politico.ng, ya dogara ne kan yanayin siyasar Najeriya kamar yadda yake ranar Talata, 1 ga Satumba, 2026.

Kara karanta wannan
Kano da wasu jihohi 19 sun fito a wuraren da Bola Tinubu zai samu nasara a zaben 2027
PIG ta tantance yadda goyon bayan al’umma yake tsakanin manyan ‘yan takarar shugaban kasa uku, inda ta sanya Atiku na jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) a matsayi na biyu.
Kungiyar ta yi hasashen cewa Atiku zai lashe jihohi tara, yayin da Peter Obi na Nigeria Democratic Congress (NDC) zai samu nasara a jihohi takwas.
Sai dai PIG ta bayyana cewa hasashen ba shi ne sakamakon karshe na zaben ba, domin yanayin siyasa na iya sauyawa sosai kafin ranar kada kuri’a.
Karfin Tinubu da Atiku a Najeriya
A karkashin hasashen PIG, Shugaba Bola Ahmed Tinubu yana da karfin gaske a Kudu maso Yamma, sannan yana samun nasara a wasu jihohin wajen yankinsa.
Wannan ya ba shi damar samun adadi mafi yawa idan aka kwatanta da sauran ‘yan takarar. PIG ta yi hasashen cewa Tinubu zai lashe jihohi 20.
A bangaren Atiku kuwa, kungiyar ta ce zai yi karfi musamman a Arewacin Najeriya, inda Kaduna da wasu jihohin Arewa maso Gabas da Arewa maso Yamma suke cikin jerin wuraren nasararsa.
Jihohin da PIG ta yi hasashen Atiku zai lashe sun hada da Sokoto, Kebbi, Niger, Katsina, Kaduna, Jigawa, Gombe, Adamawa da Taraba.
PIG ta danganta karfin Atiku a Arewa da dimbin hanyoyin sadarwarsa na siyasa da kuma gogewarsa wajen yakin neman zaben shugaban kasa a baya.
Matsayinsa kan tallafin man fetur na iya taka muhimmiyar rawa, saboda Atiku ya yi kira da a sake duba manufar yanzu tare da rage nauyin farashin fetur ga ‘yan Najeriya.
Idan farashin sufuri da tsadar rayuwa suka ci gaba da zama manyan matsaloli kafin 2027, wannan matsayar na iya jan hankalin masu kada kuri’ar da ke neman saukin rayuwa.
Sai dai PIG ta yi gargadin cewa batun tallafin man fetur ya fi alkawarin rage farashin fetur rikitarwa.
Abubuwan da za su iya sauya hasashen
PIG ta jaddada cewa bai kamata a dauki wannan hasashe a matsayin sakamakon karshe na zaben 2027 ba.
Zaben yana nan gaba, don haka akwai isasshen lokaci da yanayin siyasa zai iya sauyawa kafin ‘yan Najeriya su kada kuri’unsu.
Tattalin arzikin kasa na iya inganta ko tabarbarewa, sabbin kawance na siyasa na iya samuwa, yayin da shaharar ‘yan takara kuma za ta iya karuwa ko raguwa.

Kara karanta wannan
INEC ta fitar da sunayen yan takarar gwamna na jihohi a zaben 2027, an canza wasu
Tinubu zai iya kare manufofin tattalin arzikin gwamnatinsa, yayin da matsayin Atiku kan tallafin man fetur zai iya zama muhimmin batu a yakin neman zabe.
A halin yanzu, hasashen PIG ya sanya Tinubu a gaba da jihohi 20, Atiku na biyu da jihohi tara, sannan Obi na uku da jihohi takwas.
Atiku ya yi alkawari kan kananan hukumomi
Mun ba ku labarin cewa Atiku Abubakar ya ce zai tabbatar da biyan kuɗaɗen ƙananan hukumomi kai tsaye idan ya zama shugaban Najeriya.
an takarar shugaban kasar na jam'iyyar ADC ya ce gwamnatinsa za ta mutunta hukuncin kotu tare da kare cin gashin kan ƙananan hukumomin Najeriya.
tiku ya zargi gwamnatin Tinubu da jinkirta aiwatar da hukuncin Kotun Ƙoli kan ‘yancin kuɗaɗen ƙananan hukumomi.
Asali: Legit.ng
