APM Ta Hutar da 'Yan Adawa, Ta Gano Dan Takarar da Zai Lallasa Tinubu a Zaben 2027
- APM ta bayyana dan takarar da ta ga ya fi cancanta ya zama ɗan takarar haɗakar jam’iyyun adawa a 2027
- Jam’iyyar ta buƙaci Atiku Abubakar, Peter Obi da sauran ‘yan takara su ajiye muradun kansu domin samar da ɗan takara guda.
- Matsayar ta jam'iyyar APM na zuwa ne yayin da kungiyar G-100 ke fafutukar ganin ta samar da dan takara daya tilo a zaben shugaban kasa na 2027
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi
FCT, Abuja - Jam’iyyar Allied Peoples Movement (APM) ta bayyana gwamnan jihar Oyo, Seyi Makinde, a matsayin ɗan takarar da ta fi so ya jagoranci haɗakar jam’iyyun adawa domin kalubalantar Shugaba Bola Tinubu a zaɓen shugaban ƙasa na 2027.
Matakin jam’iyyar ya zo ne gabanin taron G-100, wata ƙungiyar siyasa da ke fafutukar samar da ɗan takarar adawa guda ɗaya da zai iya kalubalantar Tinubu a zaɓen.

Kara karanta wannan
APC: 'Dalilin Atiku na yin alkawarin dawo da tallafin man fetur idan an zaɓe shi'

Source: Facebook
APM ta yi kira ga ‘yan adawa
Sakataren Yada Labarai na Ƙasa na APM, Abubakar Yusuf, ya buƙaci sauran ‘yan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyun adawa su ajiye burinsu na kansu tare da mara wa Makinde baya, cewar rahoton The Punch.
Abubakar Yusuf ya bayyana hakan ne ranar Litinin, 24 ga watan Agustab 2026 a Abuja yayin da yake magana da manema labarai, inda ya ce tattaunawar da ake yi tsakanin jam’iyyun adawa kan samar da ɗan takara guda tana samun ci gaba.
“Zan iya tabbatar muku cewa tattaunawa da shawarwari tsakanin jam’iyyun adawa suna tafiya yadda ya kamata kuma suna kaiwa wani mataki na gaba kan batun ɗan takara guda na shugaban ƙasa."
“Ba tare da nuna bambanci ga sakamakon shawarwarin ba, Gwamna Makinde yana ƙara bayyana a matsayin mafi kyawun ɗan takarar da zai iya samun goyon bayan adawa.” In ji shi.
Atiku da Obi na neman tikiti
Yunkurin samar da ɗan takara guda na adawa na fuskantar ƙalubale, musamman saboda rahotannin cewa magoya bayan Atiku Abubakar da Peter Obi ba sa son ajiye burin ‘yan takaransu.
Sai dai Yusuf ya ce abin da ya fi muhimmanci shi ne jam’iyyun adawa su haɗa ƙarfi domin kafa gagarumar ƙungiyar siyasa da za ta kalubalanci jam’iyyar APC mai mulki.
Ya ce abin da ‘yan Najeriya ke so shi ne ganin jam’iyyun adawa sun haɗa kai domin samun sauyin shugabanci a 2027.
Dalilin goyon bayan Makinde
APM ta danganta goyon bayanta ga Makinde da yadda take ganin ya gudanar da mulkin Oyo, da kuma tasirinsa a tsakanin matasa, kwararru da sauran ɓangarorin al’umma.
Abubakar Yusuf ya ce idan aka zagaya ƙasar ana tambayar ‘yan Najeriya abin da suke so, za a gano cewa suna neman sabon salo na shugabanci mai kawo dabaru da mafita.
Ya ce Makinde na da tsarin da jam’iyyar ta yi amanna zai taimaka wajen magance matsalolin tsaro, tattalin arziki da ababen more rayuwa.
“Shi ne ɗan takara guda da ke da tsarin tabbatar da tsaron ƙasa, farfaɗo da tattalin arziki, samar da sababbin ayyukan yi da kuma farfaɗo da ababen more rayuwa,” in ji shi

Source: Facebook
Shawarar Gwamna Makinde ga 'yan adawa
A wani labarin kuma, kun ji cewa Seyi Makinde, gwamnan Oyo kuma dan takarar shugaban kasa na Allied Peoples Movement (APM), ya yi muhimmin kira ga 'yan adawa a Najeriya.
Seyi Makinde ya bukaci jam’iyyun adawa su hada kai domin bai wa ‘yan Najeriya sahihin zabin siyasa a zaben 2027.
Asali: Legit.ng

