ADC Ta Fito da Bayani, An Ji Dalilin Atiku na Kin Sa Hannu a Yarjejeniyar Zaman Lafiya Ta Zaben 2027
- Jam'iyyar ADC ta yi karin haske kan rashin ganin Atiku Abubakar a taron rattaba hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya a zaben 2027
- Jam’iyyar ta ce Kwamitin Zaman Lafiya na Kasa bai ɗauki matakin da ya dace kan tashe-tashen hankulan siyasa da ke faruwa ba
- Bolaji Abdullahi ya ce ya kamata a riƙa ɗaukar ’yan siyasa da alhaki kan kalaman da za su iya haddasa tashin hankali
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Abuja, Nigeria - Jam’iyyar ADC ta kare rashin halartar ɗan takararta na shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, wajen rattaba hannu kan Yarjejeniyar Zaman Lafiya ta Ƙasa.
Ta bayyana cewa matakin ya kasance wata hanya ce ta nuna rashin amincewa da abin da ta bayyana a matsayin gazawar tsarin zaman lafiyar wajen magance tashin hankalin zaɓe.

Source: Facebook
Sakataren Yaɗa Labarai na Ƙasa na jam’iyyar, Bolaji Abdullahi, ne ya bayyana hakan ne ranar Juma’a yayin wata hira a shirin Sunrise Daily na Channels Television.
Ya ce ADC ta yanke shawarar kin halartar bikin rattaba hannun ne da gangan, yana mai cewa ’yan siyasa sun sha rattaba hannu kan irin waɗannan yarjejeniyoyi a lokutan zaɓe da suka gabata ba tare da ganin an ɗauki mataki idan an saba ba.
Jam'iyyar ADC ta yi tir da tsarin
“Mun kasance muna rattaba hannu kan wannan abu shekara bayan shekara, a kowane lokacin zaɓe; muna rattaba hannu don nuna goyon bayan wannan alƙawari.
"Amma abubuwa har yanzu suna faruwa; ana kashe mutane, ana gallaza musu, kamar yadda ya faru a Osun, amma ba mu ji Kwamitin Zaman Lafiya ya ce komai ba. Ba sa yin Allah wadai da kisan.”
- Bolaji Abdullahi.
Abdullahi ya kuma yi tsokaci kan kalaman da aka danganta ga Sanatan Osun, Francis Fadahunsi, gabanin zaɓen gwamnan jihar da aka gudanar kwanan nan, yana mai cewa kwamitin bai dauki matakin da ya kamata ba.
“Lokacin da Sanata Fadahunsi ya ce su fita su kashe mutane, ba mu ji Kwamitin Zaman Lafiya ya ce komai ba. To, mene ne amfanin hakan? Saboda haka, wannan ita ce hanyar da mu (ADC) muka ce a’a,” in ji kakakin ADC.

Source: Twitter
ADC ta bukaci a dauki mataki
Ya ce matsayin jam’iyyar na da nufin matsa wa Kwamitin Zaman Lafiya na Ƙasa, wanda ya shirya yarjejeniyar, lamba domin ya wuce shirya bukukuwan rattaba hannu kawai, cewar rahoton Leadership.
A cewarsa, ya kamata a ɗauki shugabannin siyasa da alhaki kan kalaman da za su iya ƙarfafa tashin hankali, ba tare da la’akari da matsayinsu na siyasa ba.
NDC ta nemi Atiku ya janye takara
A wani labarin, kun ji cewa jam'iyyar adawa ta NDC ta bukaci dan takarar shugaban kasa na ADC, Atiku Abubakar ya hakura da takara a babban zaben 2027.
NDC ta bukaci tsohon mataimakin shugaban kasar ya marawa dan takararta, Peter Obi baya domin hada karfi da karfe wajen kayar da Shugaba Bola Ahmed Tinubu a zabe mai zuwa.
Asali: Legit.ng

