Jamilu Gwamna Ya Fada wa Pantami da Sauran ‘Yan takara yadda Ake Cin Zabe

Jamilu Gwamna Ya Fada wa Pantami da Sauran ‘Yan takara yadda Ake Cin Zabe

  • Dandalin sada zumunta hanyoyin sadarwa ne kawai, amma ba ya maida farin jinsu ya zama kuri'u a zabe
  • Wannan ce hudubar da Ibrahim Shawai ya yi wa masu neman takarar gwamnan jihar Gombe a shekara mai zuwa
  • Ubangidan Shawai wato Jamilu Gwamna zai kece raini da ‘yan takara kamar su Isa Ali Ibrahim Pantami

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

M Malumfashi ya shafe shekaru 10 yana kawo labaran Hausa musamman na siyasa, addini, tarihi, wasanni da al’ada

Gombe - Ibrahim Shawai hadimi ne ga Jamilu Isyaku Gwamna, ya yi magana game da abin da yake kai ‘yan takara ga nasara.

Jamilu Isyaku Gwamna shi ne ‘dan takaran APC a zaben sabon gwamnan Gombe, zai gwabaza da irinsu Isa Ali Ibrahim Pantami.

Gwamna
Mai takarar gwamna a Gombe, Jamilu Isyaku Gwamna a shekarun baya Hoto: Jamilu Isyaku Gwamna
Source: Facebook

Hadimin Jamilu Gwamna ya saki maganganu

Jaridar Punch ta kawo rahoton Ibrahin Shawai yana cewa a rumfar zabe za a goge raini a zaben 2027 ba a dandalin sada zumunta ba.

Kara karanta wannan

Zaben Gwamna: Abubuwa 5 da za su iya taimakon APC ta karbe jihar Osun

Bayanin Malam Ibrahim Shawai ya fito ne a ranar Juma’a, lokacin da yake magana game da nasarorin da Jamilu Gwamna yake samu.

Hadimin yana ganin mai gidansa yana kara samun karbuwa gabanin zaben gwamna da za a yi a jihar Gombe a farkon shekarar badi.

Ya ce duk da dandalin sada zumunta suna da muhimmanci a yau wajen tallata takara, sai dai farin jini a kafofin bai nufin yin nasara a zabe.

"Akwai wani muhimmin lamari na gaskiya game da siyasa; dokin shafukan sada zumunta a yau yana suna sa mu manta; ba a yanar gizo ake cikin zabe ba.
"Ana lashe zabe ne ta hanyar mutanen da suka fito rumfar zabe su kada kuri’arsu."

- Ibrahim Shawai

Jawabinsa ya cigaba da cewa ba a Facebook, X, Instagram ko kuwa Tik Tok za a zabi wanda zai mulki mutanen jihar Gombe a 2027 ba.

Kara karanta wannan

Muhimman abubuwan sani 11 kan jihar Osun yayin da ake gudanar da zaben gwamna

Shawai yake cewa samun karbuwa a shafukan sada zumuntan ba zai taba maye gurbin samun goyon bayan al’umma a garuruwa ba.

Ya ce:

“A 2027, ba a Facebook, X, Instagram ko TikTok za a zabi sabon gwamna na jihar Gombe ba.
"A rumfunan zabe da ke fadin kananan hukumomin jihar Gombe mutane za su dauki wannan mataki."

- Ibrahim Shawai

Gombe
'Dan takaran PDP a zaben gwamna tare da masoyansa a Gombe Hoto: Prof. Isa Pantami Foundation PIP
Source: Facebook

Abin da yake taimakon Jamilu Gwamna a Gombe

Sannan ya tuna wa jama’a cewa gwaninsa ya fi shekaru 20 yana neman zama gwamna. Sai dai 'dan siyasar bai taba yin galaba a zabe ba.

Shawai ya kuma ce aikin da Gwamna ya yi a gwamnati, kamfanoni, harkokin siyasa da taimakon marasa karfi sun taimaka masa a jihar.

Gwamna sun ziyarci Sanatan Gombe

A kwanaki aka ji labari Gwamnan Gombe, shugaban APC na kasa da Dr Jamilu Gwamna sun ziyarci Sanata Bayero Nafada na jam'iyyar PDP.

Ma girma Inuwa Yahaya, da ɗan takarar gwamna na jam'iyyar APC, Jamilu Gwamna, sun kai ziyara gidan tsohon sanaan ne domin samun goyon baya.

APC tana son hada-kai da Sanata Usman Bayero Nafada na jam'iyyar PDP domin neman kuri'u da ƙarfafa APC gabanin zaɓen da za a yi a 2027.

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng