Obasanjo Ya Tsame Kansa kan Zargin Kifar da Tsohon Gwamna, Ya Saka Sunan Atiku
- Tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo ya yi karin haske kan zargin kayar da tsohon gwamna a 2003
- Obasanjo ya zargi tsohon mataimakinsa Atiku Abubakar da shirya yunkurin tsige shi tare da yin aiki domin hana sake zabensa a 2003
- Ya ce siyasa ba ta kamata ta lalata dangantaka ba, yana mai jaddada cewa hadin kan kasa ya fi siyasar kabilanci muhimmanci
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.
Abuja - Tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo ya bayyana gaskiya kan zarginsa a zaben shekarar 2003.
Obasanjo ya yi watsi da ikirarin tsohon gwamnan Ogun, Olusegun Osoba, cewa ya yaudari shugabannin jam'iyyar AD kafin zaben shekarar 2003.

Source: Twitter
Hakan na cikin martaninsa mai taken "Reply to Your Inaccurate Posture: 'How Obasanjo Deceived Us in 2003'", cewar Punch.
Obasanjo ya kare kansa kan zargin tsohon gwamna
Ya bayyana zargin a matsayin marar tushe kuma mai cike da kuskure, inda ya ce bai taba yaudarar kowa ba, ya ce kullum yana bayyana matsayinsa da gaskiya ba tare da boye wani abu ba.
Ya ce Osoba bai san wasu muhimman tattaunawar siyasa da suka gudana tsakaninsa da shugabannin Afenifere da AD ba, domin manyan dattawan kungiyar ne suka jagoranci wadannan shawarwari.
Obasanjo ya kare sakamakon zaben gwamnoni na Kudu maso Yamma a 2003, inda PDP ta lashe jihohi biyar daga cikin shida.
Sai dai ya yi ikirarin cewa a wata jiha daya an sauya sakamakon zabe ba bisa ka'ida ba, ya kuma ce Osoba bai gudanar da yakin neman zabe sosai ba, har ya nemi afuwar jama'ar Ogun a wani shirin talabijin.
Zargin da Obasanjo ke yi wa Atiku
Tsohon shugaban kasar ya kuma zargi tsohon mataimakinsa Atiku Abubakar da shirya yunkurin tsige shi ta hannun marigayi kakakin majalisar wakilai, Ghali Na'Abba.
A cewarsa, Atiku ya gayyaci Na'Abba zuwa ofishinsa yayin da yake wajen aiki, sannan ya ba shi Naira miliyan biyar domin fara shirin tsige shi.
Obasanjo ya ce jami'in leken asirin da ke shugabancin ma'aikatansa ne ya sanar da shi hakan, cewar TheCable.
Ya kara da cewa bayan shirin tsige shi ya gaza, Atiku ya sake kokarin kulla yarjejeniya da gwamnonin AD shida domin su mara masa baya a zaben shekarar 2007.
Obasanjo ya ce an yaudari gwamnonin AD da cewa shi ne ke goyon bayan wannan shiri, alhali bai taba amincewa da irin wannan tsari ba.

Source: Twitter
Obasanjo ya tuna mulkinsa a 1999
Tsohon shugaban kasar ya kare matakin da ya dauka na bai wa wasu 'yan AD mukamai a gwamnatinsa bayan ya hau mulki a 1999, yana mai cewa manufarsa ita ce hada kan kasa, ba rauni ba.
Ya ce bai yarda gwamnoni shida na adawa za su iya rinjayar shugaban kasa ba, musamman ganin yana da goyon bayan gwamnoni talatin, majalisar dokoki da majalisar zartarwa.
Duk da sabanin siyasar da suka yi, Obasanjo ya yabawa Osoba saboda ware filin da aka gina dakin karatun Olusegun Obasanjo a Abeokuta, yana mai cewa wannan na daga cikin manyan gudummawar da ya bayar ga Ogun.
Obasanjo ya magantu kan sake yakin basasa
Mun ba ku labarin cewa tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo ya yi gargadi cewa Najeriya ba za ta iya fuskantar wani yaƙin basasa na biyu ba bayan wanda aka yi a baya.
Olusegun Obasanjo ya ce har yanzu ba a magance wasu daga cikin matsalolin da suka haifar da yaƙin basasa daga 1967 zuwa 1970 a Najeriya ba.
Haka zalika ya yabawa waɗanda suka tattara tarihin kisan gillar Asaba, yana mai cewa hakan zai taimaka wajen hana sake faruwar irin haka a nan gaba.
Asali: Legit.ng


