Mace Ta Samu Shiga Tikitin Takarar Shugaban Kasar Najeriya a Zaben 2027
- LP ta bayyana Bintu Konto a matsayin 'yar takarar mataimakin shugaban kasa don zaben shekara ta 2027
- Macen ‘yar siyasar za ta kasance a tikiti tare da dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar, Dr. Chibuzo Okereke
- Hajiya Bintu Konto kwararriya ce a fannin lafiyar jama'a da ayyukan jin kai mai gogewar sama da shekaru 30
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Abuja - Jam’iyyar hamayya ta LP ta gabatar da Hajia Bintu Konto a matsayin ‘yar takara a babban zabe mai zuwa na 2023.
Hajia Bintu Konto za ta yi wa jam’iyyar LP takarar mataimakiyar shugabanr kasa kuma a halin yanzu an tallata wa duniya ita.

Source: Facebook
Shugaban ERGAF-AFRICA ya samu takara a LP
A ranar Laraba, Daily Trust ta rahoto cewa an gabatar da Bintu Koko a matsayin abokiyar gamin Chibuzo Sunday Okereke.
Dr. Chibuzo Sunday Okereke wanda malamin jami’a ne a Abuja ya zama ‘dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar LP a watan jiya.
Jam’iyyar LP mai adawa tana sa ran Bintu Koko za ta taimaka mata a zaben 2027, ta ba ta kwarin guiwar ganin bayan mulkin APC.
An yi wani zama da shugabannin jam’iyyar LP na kasa a lokacin da aka gabatar da ‘yar takarar mataimakiyar shugaban na Najeriya.
Jam'iyyar LP ta tabbatar da takarar Bintu Konto
Nenadi Usman wanda ita ce shugabar LP ta kasa, ta ce an zabi Bintu Konto ne saboda adalcin jam’iyyar da ganin ana tafiya da kowa.
Zaben mace ta nemi kujerar mataimakin shugaban kasa ya yi daidai da tambarin LP mai dauke da hoton uba, uwa da kuma ‘dansu.
Tsohuwar sanatar ta Kaduna ta ce jam'iyyar LP ta yi imani da ba mata dama irin na maza a siyasa.
A game da ‘yar takarar tasu kuwa, Nenedi ta ce shugaba ce mai nagarta da ta yi fice wajen ayyuka na taimaka ‘dan adam a Najeriya.
Idan ta kai labari, shugabar jam’iyyar LP tana ganin Konto za ta kawo cigaba mai ma’ana wajen shugabanci tar da Chibuzo Okereke.

Source: Twitter
Jaridar Daily Post ta ce Gwamnan jihar Abia sai da ya samu yabo wajen shugabar jam’iyyar yayin gabatar da ‘yar takarar a birnin Abuja.
Nenedi ta yi misali da aikin gwamnatin Alex Otti a Abia, take cewa abin da za a gani kenan idan jam'iyyar LP ta karbi mulkin kasa a 2027.
Shi ma Okereke ya ji dadin yadda aka dauko masa Hajiya Konto, ya yi farin cikin aiki da ita.
‘Dan takarar na shugaban kasa yake cewa dole akwai rawar da mata za su taka, ya ce yin mulki babu su tamkar tafi ne da hannu guda.
Peter Obi ya hadu da Patrick Egloff
Ana da labarin maganar da aka yi game da Arewa maso yammacin Najeriya a zaman Peter Obi da Jakadan kasar Switzerland
Peter Obi ya gana da Jakadan Switzerland a Najeriya, Patrick Egloff, an yi zancen yadda za a taimaki mutanen kasar nan.
'Dan takarar shugaban kasar na NDC ya gode wa yadda kasar Turan ta taimaka wa Najeriya da gudumuwar da za a iya badawa.
Asali: Legit.ng

