Kudu maso gabashin Najeriya
Wasu ‘yan bindiga sun sace Francis Igwe wanda shi ne mahaifin tsohon mataimakin gwamnan Ebonyi, Dr. Kelechi Igwe, a safiyar Lahadi a Ndufu-Alike.
Gwamnan Delta, Sheriff Oborevwori, ya bayyana rasuwar tsohon mataimakin gwamna, Chif Benjamin Elue, a matsayin babban rashi ga jihar da Najeriya.
Gwamna Fintiri na Adamawa ya koma APC yau 27 ga Fabrairu, 2026. APC yanzu tana da jihohi 30, yayin da PDP ta rage jihohi 3 kacal (Oyo, Bauchi, Zamfara) a Najeriya.
'Yan sandan Ondo sun kama "fastocin boge" 6 da suka yi amfani da mu'ujizojin ƙarya don damfarar mutane. Rundunar ta bayyana matakin da za ta dauka kansu.
Gwamna Fubara ya naɗa Dagogo Wokoma a matsayin sakataren gwamnatin jiha da Sunny Ewule a matsayin shugaban ma'aikatan gwamnati, bayan sulhun Tinubu.
NiMet ta ce za a samu ƙura mai kauri a Arewa maso Gabas da wasu sassan Arewa, yayin da ake hasashen tsawa da ruwan sama a wasu jihohin Kudancin Najeriya.
Majalisar Dinkin Duniya ba ta bayar da wa’adin kwanaki 60 ba ga Najeriya kan sakin Nnamdi Kanu. Binciken da aka yi ya gano babu hujja da ke tuntsira wannan ikirari.
Peter Obi da jiga-jigan ADC sun tsallake yunƙurin kisan gilla a Benin, Jihar Edo yau 24 ga Fabrairu, 2026. Mahara sun buɗe wuta a gidan Odigie-Oyegun.
Gwamnatin Enugu ta saka harajin ₦150m ga ƴan takara don neman izinin tallan yaƙin neman zaɓe. ENSSAA ta ce dole ne a biya kuɗin kafin fara kamfen na 2026 da 2027.
Kudu maso gabashin Najeriya
Samu kari