Gwamna Abba Ya Kafa Kwamitin da Zai Tsara Masa Manufofin Tazarce a Mulkin Kano
- Gwamnan Jihar Kano, ya kaddamar da wani kwamiti mai mutum 16 domin tsara sabon shiri na yakin neman zabensa
- Kwamitin da ke karkashin jagorancin Dr. Aminu Magashi Garba, zai duba aiwatar da alkawuran da aka dauka a 2023
- Alhaji Abba Kabir Yusuf ya Asma'u Jibrin, Dr. Bashir Muzakkar, da Hon. Sunusi Bature Dawakin Tofa a cikin kwamitin
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
M. Malumfashi ya shafe shekaru 10 yana kawo labaran Hausa musamman na siyasa, addini, tarihi, wasanni da al’ada
Kano - Gwamna Abba Kabir Yusuf ya kaddamar da kwamitin da zai tsara masa manufofin yakin neman zaben da zai shiga a farkon badi.
Kwamitin nami mutum 14 zai duba yadda aka aiwatar da manufofin da Alhaji Abba Kabir Yusuf ya gabatar wa jama’a a zaben 2023.

Source: Facebook
Sanar da kwamitin tsara manufofin 2027
Darektan yada labaran gidan gwamnatin Kano, Sunusi Bature Dawakin Tofa ya fitar da sanarwa a Facebook mai dauke da bayanin.
Alhaji Sunusi Bature Dawakin Tofa ya ce wannan kwamiti zai yi aikin da zai jagoranci inda gwamnatin Abba za ta sa gaba bayan zabe.
An sanar cewa kwamitin kwararrun zai yi aiki a karkashin jagorancin Dr. Aminu Magashi Garba da Dr. Yusuf Ya’u Gambo a matsayin sakatare.
Mai girma gwamna Abba Kabir Yusuf da mataimakinsa Alhaji Murtala Sule Garo za su rika lura da duk aikin da kwamitin yake yi.
Baya ga kwararren likitan da zai jagoranci aikin, akwai shi kan shi Mai bada shawara kan harkar kiwon lafiya kuma likitan gwamna.
Mata 3 sun shiga cikin kwamitin
Kwamitin yana kunshe da shi kan shi kakakin gwamna wato Sanusi Dawakin Tofa da mata uku da za su tsara ayyuan da za ayi wa jama'a.
Cikin sunayen akwai mata irinsu Nana Asmau Jibrin da Halima Umar Sani, malamar harshen Hausa daga jami’ar Bayero ta Kano.
Wata mace a cikinsu ita ce mai taimaka wa gwamna kan ilmin mata, Injiniya Yasmin Mukhtar.
A bangaren matasa kuma akwai Muhammad Nazir Halliru, shugaban Kan-Invest da shugaban KASITDA, Dr. Bashir Abdu Muzakkar.

Kara karanta wannan
Kurunƙus: Tinubu ya mika fam ga APC, ya zabi wanda zai masa mataimaki a zaben 2027
Akwai kwararru kamar Dr. Kabiru Shehu, Barr. Musa Lawan Abdullahi, Dr. Nasiru Alasan Kabo da Dr. Kabiru Ibrahim Getso.
Wannan kwamiti ya kunshi shugabannin hukumomin KNARDA da KASCO da shugaban karamar hukumar Ajingi mai-ci.
Wani hadimin gwamnan Kano, Salisu Yahaya Hotoro ya fitar da sanarwar a shafinsa na Facebook.
Cikakken jerin ‘yan kwamitin tsara manufofin tazarce
1. Dr. Aminu Magashi Garba
2. Dr. Ibrahim Musa
3. Mallam Haladu Muhammad
4. Hon. Sunusi Bature Dawakin Tofa
5. Muhammad Nazir Halliru
6. Nana Asma’u Jibrin
7. Dr. Bashir Abdu Muzakkar
8. Dr. Farouk Kurawa
9. Kabiru Sani Yakubu
10. Dr. Yusuf Ya’u Gambo
11. Dr. Abdulhadi Zubairu Chula
12. Engr. Yesmin Mukhtar
13. Dr. Halima Umar Sani
14. Dr. Kabiru Shehu.
15. Barr. Musa Lawan Abdullahi.
16. Dr. Nasiru Alasan Kabo.
17. Dr. Kabiru Ibrahim Getso.
Tsofaffin ciyamomi da kansiloli sun ce sai Abba
Wata ƙungiyar tsofaffin Shugabannin Ƙananan Hukumomi da Kansiloli waɗanda suka yi aiki a shekarun 1997/1998 sun bi bayan Abba Kabir Yusuf.
An ji labari cewa sun zo ofishinsa domin nuna goyon baya ga Gwamna Abba Kabir Yusuf kuma su na rokon a biya su hakkoinsu kamar yadda aka yi wa wasu.
Kwamishinan yada labarai, Ibrahim Waiya wanda shi suka ziyarta dama, ya ba su N3m ya kuma yi alkawarin zai kai sauran roƙe-roƙensu ga gwmna.
Asali: Legit.ng

