Kotu Ta Ci Tarar Dan Takarar Gwamna a ADC Miliyoyi kan Fastocin Siyasa a Adamawa
- Kotun Majistare da ke Yola ta ci tarar ɗan takarar gwamna a jam'iyyar ADC na 2027 kan manna fastocin siyasa
- Kotun ta bayyana cewa shari'ar ba ta ci gaba a matsayin laifi ba, domin ba a gurfanar da wanda ake ƙara ba, ba a karanta masa tuhuma ba
- Hukumomin Adamawa sun ce hukuncin zai zama gargaɗi ga 'yan siyasa, suna jaddada cewa yaƙin neman zaɓe dole ya mutunta dokokin muhalli da tsara birane
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.
Yola, Adamawa - Dan takarar gwamna karkashin jam'iyyar ADC mai adawa ya gamu da fushin wata kotu kan lika fastocin siyasa.
Kotun Majistare ta 2 da ke Yola ta ci tarar ɗan takarar gwamnan jam'iyyar ADC na zaɓen 2027 a Adamawa, Omar Suleiman, Naira miliyan uku.

Source: Facebook
Rahoton TVC News ya tabbayar da cewa an ci tarar dan siyasar ne saboda liƙa fastocin yaƙin neman zaɓe.
Kotun ta ce an liƙa fastocin a kan gine-ginen gwamnati da wuraren jama'a a babban birnin Adamawa, abin da ya saɓa wa dokokin muhalli da tsara birane.
Babban Alƙali Musa Adamu ne ya yanke hukuncin bayan ƙarar da Ma'aikatar Muhalli ta Adamawa, Hukumar Tsara Birane da Babban Lauyan Adamawa suka shigar.
Kotun ta bayyana cewa duk da an fara shigar da ƙarar a matsayin ta laifi, daga baya an mayar da ita shari'ar gudanarwa saboda wanda ake ƙara bai halarci kotu ba.
Alƙalin ya ce ba a gurfanar da Omar Suleiman ba, ba a karanta masa tuhuma ba, sannan ba a karɓi amsa daga gare shi ba kafin zaman kotun.
Lauyan Omar Suleiman, Barista Bala Sanga, ya shaida wa manema labarai cewa kotun ta yanke hukuncin tara ta gudanarwa ta Naira miliyan uku saboda liƙa fastoci ba bisa ƙa'ida ba.
An zargi fastocin ɗan takarar da bayyana a wurare kamar Unity Flyover, Jippu-Jam Roundabout da Mai Doki Roundabout, abin da ya saɓa wa umarnin zartarwa kan tallace-tallace.
Hukumomi sun ce hukuncin zai zama gargaɗi ga masu siyasa kafin fara yaƙin neman zaɓen 2027, tare da jaddada cewa dole a mutunta dokokin muhalli da tsara birane.
Karin bayani na tafe.....
Asali: Legit.ng
