Abdulaziz Yari Ya Shirya Daukar Nauyin Zanga Zangar Adawa da Tinubu? Gaskiya Ta Fito

Abdulaziz Yari Ya Shirya Daukar Nauyin Zanga Zangar Adawa da Tinubu? Gaskiya Ta Fito

  • Kafofin sadarwa sun cika da wasu rahotanni da ake yaɗawa game da tsohon gwamnan Zamfara, Abdulaziz Yari
  • Sanata Yari ya yi karin haske kan zargin cewa yana daukar nauyin zanga-zangar adawa da gwamnatin Shugaba Bola Tinubu
  • Babban mai taimaka masa, Abdullahi Tsafe, ya ce Yari ya dade yana goyon bayan Tinubu tun kafin ya zama shugaban kasa

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Gusau, Zamfara - Tsohon gwamnan Zamfara, Abdulaziz Abubakar Yari, ya yi martani kan zargin ɗaukar nauyin zanga-zangar adawa da Bola Tinibu.

AbdulazizYari ya nesanta kansa daga wata zanga-zangar da ake shirin yi domin nuna adawa da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Yari ya musanta adawa da gwamnatin Tinubu
Shugaba Bola Tinubu da Sanata Abdulaziz Yari. Hoto: Asiwaju Bola Tinubu, Abdulaziz Yari.
Source: Twitter

Hadimin Abdulaziz Yari ya karyata jita-jitar zanga-zanga

Babban mai taimaka masa, Abdullahi Tsafe, ya bayyana a wata sanarwa da Punch ta samu.

Kara karanta wannan

Davido: Malamin Musulunci ya yi wa Rarara wankin babban bargo kan tsaro

Sanarwar ta bayyana cewa zargin da ke cewa Yari na daukar nauyin ko tallafa wa zanga-zangar adawa da gwamnati karya ne.

Tsafe ya bayyana zargin a matsayin marar gaskiya, mai cike da mugunta da kuma wanda aka shirya saboda dalilan siyasa, yana mai cewa Yari ba shi da wata alaka da zanga-zangar.

Ya ce:

“A bayyana karara ne cewa Sanata Abdulaziz Abubakar Yari ba shi da wata alaka ko kadan da duk wata zanga-zangar da ake shirin yi."

Ya kara da cewa zargin ya samo asali ne daga masu yada bayanan karya da kuma kokarin bata sunan dan siyasar.

A cewarsa, babu wani dalili da zai sa Yari ya dauki nauyin zanga-zanga kan gwamnatin da ya dade yana goyon baya tare da taimakawa wajen karfafa ta.

Dangantakar Yari da Shugaba Bola Tinubu

Tsafe ya ce dangantakar Yari da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta ginu ne bisa mutunta juna, akida ta siyasa da kuma kudurin ganin Najeriya ta samu ci gaba da kwanciyar hankali.

Ya bayyana cewa Yari ya mara wa burin Tinubu na zama shugaban kasa baya tun kafin nasararsa, inda ya zuba dimbin albarkatu da karfin siyasa domin cimma hakan.

Kara karanta wannan

An bukaci Shugaba Tinubu ya ayyana wani shirin watanni 6 don magance matsalolin Najeriya

Sanarwar ta ce Tinubu ya sha yabawa Yari a bainar jama’a saboda biyayyarsa, goyon bayansa da gudummawar da ya bayar ga nasarar jam’iyyar APC.

Tsafe ya ce ba zai yiwu mutum da ya bayar da irin wannan gudummawa ya juya ya fara tallafa wa zanga-zangar da za ta iya raunana gwamnati ba.

Ya kuma zargi masu yada labarin da kokarin bata sunan Yari da kuma yada bayanan da ba su da tushe.

A cewarsa, Yari mutum ne mai kishin kasa wanda bai taba shiga harkokin neman daukaka ta hanyar dabarun siyasa marasa kyau ba.

Ya kara da cewa falsafar siyasarsa ta kasance mai dogaro da tattaunawa, fahimtar juna da kuma bin tsarin dimokuradiyya wajen warware matsaloli.

Tsafe ya ce wasu mutane sun fara nuna damuwa kan karuwar tasirin siyasar Yari da kuma kyakkyawar alakarsa da manyan masu ruwa da tsaki a fadin kasar.

Saboda haka, ya ce ba abin mamaki ba ne idan wasu ke kokarin kirkirar cece-kuce domin janyo masa matsala ta siyasa.

Ya jaddada cewa Yari na nan daram wajen goyon bayan gwamnatin Tinubu kuma yana ganin kalubalen kasar na bukatar hadin kai, hakuri da tattaunawa mai amfani.

Kara karanta wannan

N70000 ta yi kadan: NLC za ta sake zama da Tinubu kan sabon mafi karancin albashi

Tsafe ya ce Yari na mayar da hankali kan ayyukansa na majalisar dattawa, jin dadin al’ummarsa da kuma kare muradun kasa baki daya.

Ya bukaci jama’a su yi watsi da rahotannin da ke danganta Yari da zanga-zangar adawa da gwamnati, yana mai cewa zarge-zargen karya ne kuma marasa tushe.

Sanarwar ta kammala da cewa babu wata farfaganda ko matsin lambar siyasa da za ta iya lalata dangantakar Yari da Tinubu ko kuma karkatar da shi daga biyayya da hidimar kasa.

Karin bayani na tafe...

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.