"Suna da Amfani": Jagoran NDC Ya Fadi Makomar Kwankwasiyya da Obidients a Jam'iyyar
- Jagoran NDC na kasa, Seriake Dickson, ya gana da madugun Kwankwasiyya, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso da wasu manyan jiga-jigan jam'iyyar
- Sanata Seriake Dickson ya nuna cewa ya gana da jiga-jigan ne domin dinke barakar da ta taso a jam'iyyar mai adawa a Najeriya
- Jagoran na NDC ya bayyana cewa kungiyoyin Kwankwasiyya da Obidients suna da rawar da za su taka a cikin sabuwar jam'iyyar
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi
FCT, Abuja - Jagoran NDC na kasa, Sanata Seriake Dickson, ya bayyana cewa yana kokarin gyara saɓani a tsakanin masu ruwa da tsaki na jam'iyyar.
Sanata Seriake Dickson ya bayyana hakan ne biyo bayan wani taro da ya yi da Rabiu Musa Kwankwaso da sauran manyan jiga-jigan jam'iyyar NDC.

Source: Twitter
Dickson ya fitar da wata sanarwa a shafinsa na X bayan ya karɓi baƙuncin Kwankwaso da mambobin shugabancin jam'iyyar a gidansa ranar Talata, 9 ga watan Yunin 2026.
Seriake Dickson ya gana da Rabiu Kwankwaso
A cikin sanarwarsa, Dickson ya ce taron wani ɓangare ne na shirin tattaunawa da ake ci gaba da yi da nufin tabbatar da jituwa tsakanin shugabannin jam'iyyar a Kano da kuma jagoran jam'iyyar na jihar, wanda kuma shi ne ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa na NDC.
Tsohon gwamnan na jihar Bayelsa ya ce saurin fitowar NDC a matsayin babbar jam'iyyar hamayya ya haifar da saɓani da kuma buri mabanbanta na neman fada a tsakanin mambobi, wanda hakan abu ne da ba za a iya kauce masa ba.
NDC na son warware rikice-rikicen gida
Sai dai, ya ce ana magance irin waɗannan ƙalubale ta hanyar tattaunawa, tuntuɓa, da kuma ba juna hakuri
“NDC ta yi gaggawar zama a matsayin babbar jam'iyyar hamayya a Najeriya, kuma kamar kowace tafiyar siyasa da ke haɓaka, saɓani da arangamar buƙatu abubuwa ne da ba za a iya kauce masu ba."
- Sanata Seriake Dickson
Jam'iyyar NDC ba ta nuna fin karfi
Dickson ya yi watsi da iƙirarin nuna fin karfi wajen zabar 'yan takara a cikin jam'iyyar, inda ya jaddada cewa NDC ta kasance tana ba da dama ga tsarin dimokuraɗiyya domin ayyana 'yan takararta a faɗin jihohi.
Ya ƙara da cewa tattaunawar da aka yi da Kwankwaso da sauran masu ruwa da tsaki ta haifar da ɗa mai ido, kuma ya nuna kwarin gwiwar cewa dukkan ɓangarorin za su ci gaba da aiki tare domin cimma muradun zaɓe na jam'iyyar.

Source: Twitter
Ya batun 'yan Kwankwasiyya da Obidients?
Jagoran na NDC ya bayyana ƙungiyoyin magoya baya na Kwankwasiyya da Obidient a matsayin muhimman rukunoni waɗanda za a haɗa mambobinsu cikin tsarin jam'iyyar a faɗin ƙasar.
Ya ce tun da farko ya karɓi wata tawaga daga ƙungiyar Obidient Movement kuma ya tabbatar musu da sanya su cikin ayyukan jam'iyyar a matakai mabanbanta.
Dickson ya ce za a faɗaɗa irin wannan tsari zuwa ga ƙungiyar Kwankwasiyya Movement da zarar an mika jjerin sunayen jagororinta ga jam'iyyar.
NNPP ta yi zargi kan Kwankwaso
A wani labarin kuma, jam'iyyar NNPP ta yi zargi kan madugun Kwankwasiyya, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, wanda ya yi mata takara a zaben 2023.
NNPP ta zargi Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, da ci gaba da shiga harkokin jam’iyyar duk da cewa ya yanke alaka da ita zuwa sabuwar jam'iyya.
Ta bayyana cewa Kwankwaso na ci gaba da yin tasiri a cikin jam’iyyar ta hannun wasu magoya bayansa da ake zargin ya bari a cikinta bayan ficewarsa.
Asali: Legit.ng


