Bayan Sukar Kalamansa a 2023, Peter Obi Ya Shawarci Matasa kan Siyasar Addini, Kabilanci
- Dan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NDC, Peter Obi, ya shawarci matasan Najeriya yayin da ake tunkarar zaben 2027
- Obi ya buƙaci matasan Najeriya su guji rarrabuwar kawuna ta hanyar ƙabilanci da addini, su rungumi haɗin kai
- Tsohon gwamnan ya ce bayan zaɓen 2023 a Lagos, tattaunawa ta karkata zuwa ƙabilanci wanda bai dace ba ko kadan
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.
Abuja - Dan takarar shugaban kasa a NDC, Peter Obi ya ba da shawara game da siyasar Najeriya.
Peter Obi ya buƙaci matasan Najeriya da su yi watsi da rarrabuwar kawuna ta ƙabilanci da addini, yana mai jaddada muhimmancin haɗin kai da makomar ƙasa.

Source: UGC
A cikin saƙon da ya wallafa a shafin X, Obi ya yi nazari kan darussan da aka koya daga zaɓen shekarar 2023, musamman a Lagos.
Gargadin da Peter Obi ya yi kan siyasa
Ya ce tattaunawar jama'a ta kauce daga batutuwan shugabanci da ci gaba zuwa na ƙabila da bambance-bambancen kabilanci.
Ya gargadi cewa irin waɗannan bayanai suna sake bayyana, tare da kira ga ‘yan Najeriya su kasance cikin shiri.
Obi ya ce wasu ‘yan siyasa kan koma amfani da ƙabila, addini da batutuwan asali idan ba za su iya yin gogayya ta fuskar tunani, aiki, hali ko hangen nesa ba.
Ya bayyana cewa mutane da dama na shiga irin waɗannan muhawarori ba tare da sanin cewa ana jan su cikin labaran da wasu suka ƙirƙira ba.
Ya ƙara da cewa wasu kamfen-kamfen na samun yaɗuwa ne ta hannun mutanen da ke tunanin suna goyon bayan kyakkyawan manufa alhali ba su fahimci wata babbar manufa da ke bayan hakan ba.

Source: Twitter
Obi ya yabawa babban fasto a Najeriya
Tsohon gwamnan Anambra ya kuma yi magana kan babban mai kula da cocin RCCG, Fasto Enoch Adeboye.
Ya bayyana Adeboye a matsayin ɗaya daga cikin manyan shugabannin Kiristoci na Najeriya wanda ya dade yana wa’azin zaman lafiya, addu’a, soyayya, sulhu da haɗin kai na ƙasa.
Peter Obi ya ce bai dace matasa su ɗora wa Fasto Adeboye mai shekaru 84 nauyin da ya rataya a wuyansu ba, ya ce babban nauyin gina Najeriya mafi kyau yana kan matasa.
Ya rubuta cewa:
“Aikin gina Najeriya mafi kyau ya rataya ne a wuyan matasa. Su ne ya kamata su jagoranci tattaunawa, su ɗauki nauyin gyare-gyare, kuma su jagoranci canjin da ƙasarmu ke matuƙar buƙata.”
Ya kuma gargadi ‘yan Najeriya da kada su zama kayan aiki a hannun masu yaɗa rarrabuwar kawuna yayin da a fili suke kiran haɗin kai.
An kwatanta tsarin siyasar Obi da ta Buhari
Mun ba ku labarin cewa masani kan harkokin siyasa ya bayyana cewa matsalolin Najeriya sun fi karfin mutum guda ɗaya duba da matsalar kasar.
Masanin harkokin siyasar nan, Sola Kuti ya bayyana cewa tsarin siyasa ne babban kalubalen da ke hana ci gaba a Najeriya.
Ya ce ko shugaba mai kyakkyawar niyya zai fuskanci cikas daga masu ruwa da tsaki da tsarin da ke hana sauye-sauye masu ma'ana.
Asali: Legit.ng

