An Fara Jita Jitar Cewa Sheikh Abdulmudallib Ya Samu Tikitin Takarar Gwamna a 2027

An Fara Jita Jitar Cewa Sheikh Abdulmudallib Ya Samu Tikitin Takarar Gwamna a 2027

  • An fara yada jita-jitar cewa jam'iyyar adawa ta ADC ta tsayar da Sheikh Abdulmudallib Muhammad takarar gwamnan Zamfara a 2027
  • Duk da ba wata sanarwa a hukumance, an ce fitaccen malamin addinin musulunci ya samu tikiti bayan amincewar shugabanni da mambobin ADC
  • Ana sa ran takararsa za ta kara zafafa fafatawar siyasa a jihar yayin da Gwamna Dauda Lawal ke neman tazarce a inuwar jam'iyyar APC

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Zamfara, Nigeria - Wasu rahotanni da ba a tabbatar ba sun nuna cewa malamin addinin Musulunci, Sheikh Abdulmudallib MuhammaD, ya samu tikitin takarar gwamna na ADC a Zamfara.

Jita-jitar ta nuna cewa jam’iyyar ta amince da malamin ne bayan tuntubar shugabanni, masu ruwa da tsaki da kuma mambobin jam’iyyar a fadin jihar da ke Arewa maso Yamma.

Kara karanta wannan

Abu ya girma: Jam'iyyar APC ta dakatar da dan majalisar tarayya daga jihar Jigawa

Sheikh Abdulmudallib.
Babban malamin musulunci, Sheikh Abdulmudallib Muhammad lokacin da ya karbi fam din takara a ADC Hoto: Sheikh Abdulmudallib Muhammad Gusau
Source: Facebook

Kafar watsa labarai ta Freedom Radio Nigeria ta bayyana hakan a wani gajeren sako da ta wallafa a shafin Facebook yau Laraba, 3 ga watan Yuni, 2026.

ADC ta fadi dalilin zaben malamin

An ruwaito cewa shugabannin jam’iyyar ADC sun bayyana cewa an zabi Sheikh Abdulmudallib Auwal ne saboda irin gudunmawar da yake bayarwa wajen wayar da kan al'umma da kuma kyakkyawan suna da yake da shi a tsakanin jama'a.

Sun ce jam’iyyar na da yakinin cewa dan takararta zai iya jan hankalin masu kada kuri’a daga bangarori daban-daban na jihar, musamman matasa da masu neman sauyi a harkokin shugabanci.

Sai dai har yanzu babu wata sanarwa a hukumance daga jam'iyyar ADC ko malamin, da ta tabbatar da wadannan rahotanni da jita-jita da ake yadawa.

Ku saurari karin bayani....

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262