2027: Tsohon Gwamnan Ebonyi Zai Jagoranci Kwamitin Tantance Masu Neman Takara a NDC
- Jam'iyyar NDC ta kafa kwamitin da zai tantance masu neman takarar shugaban kasa, gwamnoni da 'yan Majalisa karkashin inuwarta a zaben 2027
- Tsohon gwamnan jihar Ebonyi, Sanata Sam Egwu, shi ne zai jagoranci wannan kwamiti, mai kunshe da mambobi 17
- NDC ta ce kwamitin ya hada shugabanni, kwararru da kuma mambobin kwamitin gudanarwa da aka zabo domin kula da aikin tantance ‘yan takara
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Abuja, Nigeria - Jam’iyyar NDC ta fara shirye-shiryen tantance yan siyasar da suka nuna sha'awar tsayawa takarar shugaban kasa, gwamnoni, sanatoci da yan Majalisar wakilai a 2027.
NDC ta nada tsohon gwamnan jihar Ebonyi, Sanata Sam Egwu, a matsayin shugaban kwamitin tantance masu neman takarar shugaban kasa, gwamnoni, sanatoci da ‘yan majalisar wakilai gabanin zaben 2027.

Source: Facebook
Jam’iyyar ta bayyana hakan ne cikin wata sanarwa da sakatarenta na kasa, Ikenna Morgan Enekweizu, ya fitar ranar Talata, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.
Sanarwar ta ce za a kaddamar da kwamitin mai mutum 17 da karfe 4:00 na yammacin ranar Talata, 19 ga watan Mayu, 2026.
Sam Egwu zai jagoranci tantance ‘yan takara
Egwu, wanda ya taba zama gwamna sau biyu a jihar Ebonyi, sannan kuma tsohon dan majalisa, zai jagoranci aikin tantance masu neman mukaman siyasa karkashin jam’iyyar NDC.
Jam’iyyar ta kuma nada mai ba ta shawara kan harkokin shari’a na kasa, Reuben Egwuaba, a matsayin sakataren kwamitin.
Sunayen sauran mambobin kwamitin
Sauran mambobin kwamitin sun hada da:
1. Babatunde Ali — mataimakin shugaban kwamitin
2. Buba Galadima
3. Mohammed Takori
4. Daniel Onifade
5. Ikeddy Isiguzo
6. Wole Adedayo
7. Dr Osusu Osusu
8. Chief Asukewe Ikoawaji
9. Prof. Udenta Udenta
10. Frederick E. Owotorufa
11. Hannatu Tanko
12. Dogo Shammar
13. Sir Henry Obaze
14. Clement Agiagie
15. Fatima Abba.

Source: Twitter
Jam’iyyar ta ce kwamitin ya kunshi shugabannin jam’iyya, kwararru da kuma mambobin kwamitin gudanarwa na kasa da aka zabo domin kula da aikin tantance ‘yan takara a zaben 2027.
NDC ta fara shirye-shiryen zaben 2027
Matakin na zuwa ne yayin da NDC ta kara zage damtse wajen shirye-shiryenta da nufin tunkarar babban zaben 2027, cewar rahoton Vanguard
A baya-bayan nan jam'iyyar NDC ta fara amfani da tsarin masalaha wajen zaben fidda gwani a wasu yankuna domin kauce wa rikice-rikicen cikin gida da kuma karfafa hadin kan jam’iyyar.
NDC ta rufe sayar da fam din takara
A wani labarin, kun ji cewa jam’iyyar hamayya ta NDC ta rufe sayar da fam na neman takarar shugaban ƙasa na babban zaben 2027.
Bayanai daga jam'iyyar sun tabbatar da cewa tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar LP a zaɓen 2023, Mista Peter Obi, ne kaɗai.ya sayi fam ɗin.
Jam’iyyar ta ce ta ƙara wa’adin karɓar fam ɗin nuna sha’awa na gwamnoni, sanatoci da yan Majalisar dokoki ta tarayya da ta jihohi da mako guda.
Asali: Legit.ng

